– Lauyan shugaban kungiyar IMN
Ibrahim Az-Zakzaky, Femi Falana ya rubuta takarda ga Osinbajo
– Lauyan ya nemi a saki shugaban
kungiyar shi’a da ke garkame
– Ana dai cigaba da daure Ibrahim
El-Zakzaky bayan tsawon lokaci
Femi
Falana SAN Lauyan shugaban kungiyar IMN Ibrahim Az-Zakzaky, ya rubuta wasika ga
Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo SAN da kuma Ministan shari’a na kasar
Abubakar Malami SAN game da cigaba da daure malamin.
Falana
yace idan har gwamnati ba ta saki Zakzaky ba zai dauki mataki. Babban Lauyan
yace zai nemi Kotu tayi watsi da karar gwamnatin tarayya da ke babban kotun
kasar da ke Abuja idan har ba a saki shugaban Kungiyar na Shi’a ba.
A
watan Disamban bara Alkali Gabriel Kolawole ya nemi a saki Ibrahim Zakzaky da
matar sa ba tare da bata lokaci ba. Alkali mai shari’ar ya kuma nemi a biya su
kudi Naira Miliyan 50 sannan kuma a gina masa wani gida cikin Garin Kaduna ko duk
inda su ke so bayan barnar da aka yi masu.
Falana
yace har yau ba ayi wannan ba kuma ana cigaba da rike Zakzaky. Babban Lauyan
yace dole a gaggauta sakin malamin ba tare da bata lokaci ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment