– Tauraron dan wasan Kasar Jamus Phillip Lahm ya ajiye kwallo
– Dan wasa ya ajiye kwallo bayan ya kafa tarihi
– Lahm
bai taba samun jan kati ba
Babban Dan wasa kuma Kyaftin
din Kasar Jamus da kuma Kungiyar Bayern Munich Philip Lahm ya bayyana cewa daga
karshen wannan shekarar zai daina taka leda. Lahm yana da shekaru 33 a yanzu
haka.
Bayan dai fiye da shekaru 20
ana murzawa dan wasan bayan yace ya gaji hakanan, zai koma gida ya huta. Lahm
ya bugawa Bayern wasanni sama da 500 sannan kuma ya bugawa kasar Jamus wasa
sama da 100 har ta kai ya rike kambu.
Lahm dai ya ci kyaututtuka
da kofuna da dama a Duniya. An kuma nemi ya zauna a Kulob din a cigaba da
damawa da shi, amma yace sam akwai gyara tukun. Tun da Lahm yake kwallo a
Duniya dai bai taba karban jan kati ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment