– Hukumar
EFCC ta karbe kusan Dala Miliyan 10 daga hannun Andrew Yakubu
– Tsohon
Manajan NNPC Andrew Yakubu yace dole a maido masa kudin sa
– Andrew Yakubu ya dai ce ba satan kudin yayi ba
Kwanakin baya wani babban
Kotun Tarayya da ke Garin Kano ya bada dama Gwamnatin tarayya ta rike makudan
kudin da aka samu daga gidan Tsohon Manajan Kamfanin main a Najeriya watau NNPC
Andrew Yakubu.
Sai dai tsohon shugaban NNPC
din ya nemi Kotu tayi watsi da hukuncin da aka yanke a baya kurum a maido masa
kudin sa. Lauyan Andrew Yakubu yana karar Kotun da ta yanke shari’ar a baya
yace babu wanda ya isa ya taba masa kudin sa.
Lauyan da ke kare Andrew
Yakubu, Ahmed Raji SAN yace ana zargin Andrew Yakubu ya saci kudin ne a Birnin
Tarayya Abuja don haka wata Kotu a Garin Kano ba ta isa tace za ta karbe kudin
ba kamar yadda dokar kasa tace.
Kwanaki ne dai Hukumar EFCC
ta samu wasu mahaukatan kudi kusan Dala Miliyan 9.8 a gidan tsohon Manajan
Kamfanin NNPC din na kasa. Andrew Yakubu dai yayi wuf yace duk kyaututtuka ne
aka rika kawo masa lokacin yana Ofis.
No comments:
Post a Comment