Monday, February 20, 2017

Babu wanda ya isa ya karbe mani daloli na-Andrew Yakubu


Hukumar EFCC ta karbe kusan Dala Miliyan 10 daga hannun Andrew Yakubu


Tsohon Manajan NNPC Andrew Yakubu yace dole a maido masa kudin sa


Andrew Yakubu ya dai ce ba satan kudin yayi ba



Kwanakin baya wani babban Kotun Tarayya da ke Garin Kano ya bada dama Gwamnatin tarayya ta rike makudan kudin da aka samu daga gidan Tsohon Manajan Kamfanin main a Najeriya watau NNPC Andrew Yakubu.

Sai dai tsohon shugaban NNPC din ya nemi Kotu tayi watsi da hukuncin da aka yanke a baya kurum a maido masa kudin sa. Lauyan Andrew Yakubu yana karar Kotun da ta yanke shari’ar a baya yace babu wanda ya isa ya taba masa kudin sa.



Lauyan da ke kare Andrew Yakubu, Ahmed Raji SAN yace ana zargin Andrew Yakubu ya saci kudin ne a Birnin Tarayya Abuja don haka wata Kotu a Garin Kano ba ta isa tace za ta karbe kudin ba kamar yadda dokar kasa tace.

Kwanaki ne dai Hukumar EFCC ta samu wasu mahaukatan kudi kusan Dala Miliyan 9.8 a gidan tsohon Manajan Kamfanin NNPC din na kasa. Andrew Yakubu dai yayi wuf yace duk kyaututtuka ne aka rika kawo masa lokacin yana Ofis.


[NAIJ Hausa]





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...