– Shugaban
kasa Muhammadu Buhari na shirin dawowa Najeriya
– Buhari ya tafi hutu Kasar Birtaniya tun watan jiya
– Zuwa
gobe Shugaban kasa Buhari zai shiga Ofis
Idan ba a manta ba Shugaba
Muhammadu Buhari ya bar Najeriya ne a Ranar 19 ga Watan Junairu inda ya tafi
hutu Kasar Birtaniya. To da alamu dai jirgin Shugaban kasar ya fara shirin
tashi don kuwa lokacin dawowan sa gida yayi.
Shugaba Buhari ya nemi
Majalisa ta san da tafiyar sa zuwa hutun inda ya kuma nemi Mataimakin sa Yemi
Osinbajo ya zama Mukaddashi har sai ya dawo. Zuwa gobe dai ake sa ran cewa
Shugaba Buhari zai shiga Ofis.
A lokacin da ba ya nan an ta
yada jita-jita iri-iri cewa Shugaba Muhammadu Buhari yam utu a can. Har sai da
ta kai an fito da hotunan sa inda yake shakatawa kana wasu su ka yarda yana
raye. Kungiyar nan ta Izalatul Bidi’a wa Iqamatus Sunnah ta Kasa ta soki masu
kirawa shugaba Buhari mutuwa. Kungiyar ta ce kowa idan lokaci yayi zai mutu.
Wata Kungiya mai suna NYCN
ta matasan Najeriya dai za ta shirya taron gangami na mutane 1500 domin
murnar dawowan Shugaba Buhari.
{NAIJ Hausa}
No comments:
Post a Comment