Wani babban jigo a jam’iyyar
APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yace yana iya tsayawa takarar shugaban kasar
nan, ko da yake dai babu wanda ya san gobe.
Tsohon Gwamnan Legas, Bola Ahmed Tinubu yace zai iya
neman kujerar shugaban kasa nan gaba. Tinubu yayi wannan magana ne a wajen
bikin rantsar da sabon Gwamnan Jihar Ondo Rotimi Akerodolu.
A wata hirar bidiyo da Tinubu yayi da Sahara Reporters
ya bayyana cewa ba zai ce a’a ba game da takarar shugaban kasa, Bola Tinubu
yace shugabanci na kasa kamar bauta ne da yi wa kasa hidima.
Bola Tinubu yace yana iya takara nan gaba don babu
abin da ya hana sa, sai dai yace hakan na iya danganta da yanayi na siyasa da
sauran su. Tinubu yace ko shugaba Muhammadu Buhari sai bayan ya cire rai ne ya
samu mulki.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment