–
Da alamu Likitocin Ingila sun fadawa shugaba Buhari ya huta tukun
– An
ba sa wannan shawara ne saboda lafiyar jikin sa
–
Yanzu haka dai Farfesa Osinbajo ke rike da kasar nan
Mun samu kishin-kishin din cewa Likitocin da ke kula
da lafiyar shugaba Muhammadu Buhari a kasar Ingila sun fadawa shugaban kasar da
ya rabu da mulkin kasar nan har sai ya samu sauki nan gaba.
Likitocin dai sun ba shugaba Muhammadu Buhari wannan
shawara ne saboda ya kula da lafiyar jikin sa kamar yadda muke samun labari
daga wata Majiya daga Jaridar Sahara Reporters ta kasar da ke Amurka.
Sai dai wasu na kusa da shugaban kasar suna kokarin
ganin shugaba Muhammadu Buhari yayi watsi da wannan shawara na Likitoci ya dawo
kurum ya cigaba da rike madafan iko na kasar. Ba mamaki Likitocin dai sun
gargadi shugaba Buhari game da dawowa ba tare da ya kammala ganin Likita ba.
Yanzu haka dai Mataimaki Farfesa Yemi Osinbajo ke rike
da kasar tun tafiyar shugaba Buhari Ingila.
An fara cewa dai har shugaban kasar ya fara rage nauyi saboda rashin
lafiyar da ke damun sa wanda har yau ba a san menene ba. Mun samu labari dai cewa Shugaba Buhari ya kara ganawa da Bukola Saraki jiya a Landan.
No comments:
Post a Comment