Monday, February 20, 2017

Likitoci sun fadawa shugaba Buhari ya huta


– Da alamu Likitocin Ingila sun fadawa shugaba Buhari ya huta tukun


– An ba sa wannan shawara ne saboda lafiyar jikin sa


Yanzu haka dai Farfesa Osinbajo ke rike da kasar nan




Mun samu kishin-kishin din cewa Likitocin da ke kula da lafiyar shugaba Muhammadu Buhari a kasar Ingila sun fadawa shugaban kasar da ya rabu da mulkin kasar nan har sai ya samu sauki nan gaba.

Likitocin dai sun ba shugaba Muhammadu Buhari wannan shawara ne saboda ya kula da lafiyar jikin sa kamar yadda muke samun labari daga wata Majiya daga Jaridar Sahara Reporters ta kasar da ke Amurka.

Sai dai wasu na kusa da shugaban kasar suna kokarin ganin shugaba Muhammadu Buhari yayi watsi da wannan shawara na Likitoci ya dawo kurum ya cigaba da rike madafan iko na kasar. Ba mamaki Likitocin dai sun gargadi shugaba Buhari game da dawowa ba tare da ya kammala ganin Likita ba.


Yanzu haka dai Mataimaki Farfesa Yemi Osinbajo ke rike da kasar tun tafiyar shugaba Buhari Ingila.  An fara cewa dai har shugaban kasar ya fara rage nauyi saboda rashin lafiyar da ke damun sa wanda har yau ba a san menene ba. Mun samu labari dai cewa Shugaba Buhari ya kara ganawa da Bukola Saraki jiya a Landan.




[NAIJ]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...