Tuesday, February 28, 2017

Tsufa ba zai sa in ajiye aiki ba-Mugabe


– Shugaban kasar Zimbabwe yace yawan shekaru ba za su sa ya ajiye mulki ba


– Shugaba Mugabe ya cika shekaru 93 a Duniya


– Mugabe yace sam bai da niyyar sauka daga mulki





Shugaban Kasar Zimbabwe Robert Mugabe yace yawan shekaru ba za su ya sa sauka daga kujerar mulki ba. Mugabe dai ya cika shekaru 93 da haihuwa a Duniya ya kuma sam bai da niyyar sauka daga mulki.

Robert Mugabe ne dai shugaban kasar da ya fi kowane dadewa a Duniya ya kuma yi shekaru 37 yana mulkin kasar Zimbabwe. Mugabe dai yayi bikin cika shekara 93 a Duniya inda ya bayyana cikin bakin tabaron sa.




Shugaba Mugabe yace bai ga ranar da zai sauka ba bayan ya dade yana shugabanci. Mugabe yace idan har zai sauka daga mulki ba zai yi kokarin kakabawa Jam’iyyar wani dan takara ba da zai yi mulki. 

Kwanaki Wani Fasto mai suna Patrick Mugadaza ya bayyana cewa shugaban na kasar Zimbabwe, Robert Mugabe zai rasu a cikin watan Oktoban wannan shekarar, ko da ya sanar da hakan sai ‘Yan Sanda suka kama shi. A Kasar Zimbabwe bai hallata kace shugaba Mugabe zai mutu.



[NAIJ Hausa]




Lauyan Zakzaky ya samu Osinbajo


– Lauyan shugaban kungiyar IMN Ibrahim Az-Zakzaky, Femi Falana ya rubuta takarda ga Osinbajo


– Lauyan ya nemi a saki shugaban kungiyar shi’a da ke garkame


– Ana dai cigaba da daure Ibrahim El-Zakzaky bayan tsawon lokaci




Femi Falana SAN Lauyan shugaban kungiyar IMN Ibrahim Az-Zakzaky, ya rubuta wasika ga Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo SAN da kuma Ministan shari’a na kasar Abubakar Malami SAN game da cigaba da daure malamin.

Falana yace idan har gwamnati ba ta saki Zakzaky ba zai dauki mataki. Babban Lauyan yace zai nemi Kotu tayi watsi da karar gwamnatin tarayya da ke babban kotun kasar da ke Abuja idan har ba a saki shugaban Kungiyar na Shi’a ba.

A watan Disamban bara Alkali Gabriel Kolawole ya nemi a saki Ibrahim Zakzaky da matar sa ba tare da bata lokaci ba. Alkali mai shari’ar ya kuma nemi a biya su kudi Naira Miliyan 50 sannan kuma a gina masa wani gida cikin Garin Kaduna ko duk inda su ke so bayan barnar da aka yi masu.

Falana yace har yau ba ayi wannan ba kuma ana cigaba da rike Zakzaky. Babban Lauyan yace dole a gaggauta sakin malamin ba tare da bata lokaci ba.



[NAIJ Hausa]

Monday, February 27, 2017

Abubuwan da Osinbajo yayi bayan tafiyar Buhari




Tun tafiyar shugaba Muhammadu Buhari kawo yanzu mukaddashin shugaban kasar Yemi Osinbajo ya dauki matakai da ayyuka da dama a kasar. A wani nazari da muka yi, mun jero manya daga ciki




Yanzu haka dai Farfesa Osinbajo ke rike da Najeriya ya kuma yi ayyuka tafiyar shugaba Buhari na a-zo-a-gani. Kadan daga ciki su ne sauyi da aka gani a tsare-tsaren harkar kudin kasar daga CBN. Farfesa Osinbajo kuma ya shiga lungunan Neja-Delta domin kwantar da rikicin da ke Yankin.

Mukaddashin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya saki kudin wasu manyan kwangiloli a Kaduna da Legas wancan makon bayan taron Majalisar FEC. Haka kuma Shugaban rikon kwaryar ya ci burin gyara tattalin arzikin Najeriya ta hanyar saukake harkar kasuwanci a kasar cikin watanni biyu.

Tun hawan sa dai ya nada Kwamiti domin ya ji dalilin da ya sa farashin abinci ya tashi a Najeriya. Farfesa Osinbajo ya kuma gana da shugabannin Majalisa ba sau daya ba, ba sau biyu ba a game da harkar kasafin kudin wannan shekarar.

Osinbajo ya kuma rattaba hannu a wasu kudirori da Majalisar ta aiko masa yayin da kuma yayi mursisi yayi watsi da wasu kudirorin tare da bayyana dalilan sa. Har a kasar waje dai ana ta kawo ziyara ga shugaban kasar na rikon karya inda shi ma ya taka har kasar Gambia wajen nadin sabon shugaba Adama Barrow.


[NAIJ Hausa] 



Ya aka yi Darajar Naira ke tashi?


– A cikin ‘yan kwanakin nan dai Naira ta tashi


– Naira tayi tashin da ba ta taba yin irin sa ba


Ko ta ya aka cin ma wannan?





Hakar babban bankin Najeriya na CBN ta fara ci wa ruwa don kuwa har abubuwa sun fara yin kyau. Kwanan nan ne dai babban bankin kasar watau CBN ya sauya tsare-tsaren sa na harkar kudin kasar bayan Mukaddashin shugaban kasa da kuma Ministan kudi sun fito sun yi magana cewa ya kamata a canza tsari.

A lokacin da aka zauna dai ana sa ran Dalar na iya zarce N600 idan ba ayi wasa ba, hakan ta sa dole aka sake sabon lale. Bayan kwanaki kadan dai sai ga CBN da sababbin manufofi wanda suka taimaka yanzu Dalar tana ta kara yin kasa.

Ko da ma can dai kudin kasar wajen Najeriya yana ta kara habaka bayan da aka hana shigo da abubuwan da ba su da wani tasiri daga kasar waje irin su farantin kwangiri da tsinken sakace. Yanzu dai asusun Najeriya na kudin kasar waje ya zarce Dala Biliyan $30. Wannan ya ba CBN damar zubo dalolin wanda da ‘yan kasuwa sun boye su.

An dai kuma dai yi katari rikici a Yankin Neja-Delta ya fara raguwa kuma gangar man Najeriya yayi tsada a kasuwa, wannan ya sa Najeriyar ta samu wasu ‘yan rara. Ko shin ya za a daure da haka?


[NAIJ Hausa] 




Dan shekara 28 ya auri mai shekaru 82


 Wani Saurayi ya auri wanda ta yi jika da shi


– An dai ce ita soyayya ba ruwan ta


Dan shekara 28 ya auri tsohuwa ‘yar 82





Da yake shi ‘so’ ba gani yake yi ba, ga dai wani matashi na dan shekara 28 ya buge da auren wanda ta girme sa da shekaru 54 a Duniya. Wannan abu dai ya faru ne a can kasar Indonesia.

Ko da yake dangin juna ba su so wannan aure ba amma aikin gama ya gama tun da masoyan suka ce sun ji sun gani. Kwanan baya ne wani matashi mai aikin kwadago Sofian Laho Dandel ya shiga soyayya da wata tsohuwa Martha mai shekaru fiye da 80 a Indonesia.  




Kamar yadda jaridar Tribune news ta kawo tace yanzu har an shirya aure duk da banbancin shekarun. Martha dai tsohuwa ce wanda ta rasa mijin ta shekaru fiye da 10 da suka wuce, ta kuma ce yanzu ita da Sofian, mutu ka raba; takalmin kaza.

Bisa dukkanin alamu dai Duniyar nan ta zo karshe don kuwa kwanaki muka samu wani labari da ba mu taba jin irin sa ba shi ma. A Kasar Zambia wani saurayi ne ya auri mahaifiyar sa bayan uban sa ya rasu.




[NAIJ Hausa]

Bola Tinubu zai tsaya takara?





Wani babban jigo a jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yace yana iya tsayawa takarar shugaban kasar nan, ko da yake dai babu wanda ya san gobe.

Tsohon Gwamnan Legas, Bola Ahmed Tinubu yace zai iya neman kujerar shugaban kasa nan gaba. Tinubu yayi wannan magana ne a wajen bikin rantsar da sabon Gwamnan Jihar Ondo Rotimi Akerodolu.

A wata hirar bidiyo da Tinubu yayi da Sahara Reporters ya bayyana cewa ba zai ce a’a ba game da takarar shugaban kasa, Bola Tinubu yace shugabanci na kasa kamar bauta ne da yi wa kasa hidima.

Bola Tinubu yace yana iya takara nan gaba don babu abin da ya hana sa, sai dai yace hakan na iya danganta da yanayi na siyasa da sauran su. Tinubu yace ko shugaba Muhammadu Buhari sai bayan ya cire rai ne ya samu mulki.



[NAIJ Hausa]









Saturday, February 25, 2017

HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN



HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN-ZARIA




Me muke nema a Duniya?-Daga Bakin Imam Sheikh S. S Abubakar


A’udhu BilLahi minasshaidan Ar-Rajim, BismilLahir Rahman Ar-Raheem,

Dukkan Godiya sun tabbata ga Allah SWT, muna rokon gafarar Sa da samun yardar Sa. Godiya da yabo sun tabbata gare shi Madaukakin Sarki. Muna shaidawa lallai babu abin bauta da gaskiya face Allah SWT, Shi kadai yake, babu abokin tarayya a gare Sa. Muna shaidawa lallai Shugaban mu, Annabi Muhammad SAW Bawan Allah ne kuma Manzon Sa ne.
Bayan Haka:
Ya dace mu rika tambayar kawunan mu bayan lokaci wai ‘shin me ‘Dan Adam yake nema a doron kasa?’ Sau da yawa sai kaji mutum yace yana son rayuwa ta farin ciki a cikin Duniya na dukiya masu dinbin yawa. Sai ka ga mutum yana ta kokari wajen samun natsuwa da hutu a cikin rayuwar Duniya. Da yawa su na neman morewa a cikin rayuwa, ko mecece morewar? Dankareren gida cike da masu hidima da motoci da sutura na alfahari da abinci mai dadi, sune abin morewar? Mafi yawanci dai abin da ‘Dan Adam yake nema kenan a rayuwa ko da bai furta hakan ba. Ko da yake ba wannan ne matsalar ba, sai dai hanyar da Jama’a ke bi wajen samun wannan rayuwar ita ce suke bacewa, su rika lalube cikin rudun su, suna masu dimaucewa, suna fadi-tashi. Irin wannan al’amari dai bai dace ya samu ‘Dan uwa Musulmi ba. Ya kai Mumuni mai tsoron Allah wanda ya tasiran tu da Imani, ai lallai kai ne ke cikin jin dadi idan har ka samu imani. Duk wanda yayi abin da ya dace da imani shi ne wanda yake jin dadin Duniya kuma zai rabota a Lahira. Hanya ta hakika guda daya da za ta kai mutum ga abin da yake buri shi ne Addinin Musulunci. Face wannan Addini babu abin da zai kai ka ga wannan buri, bari ganin irin abin da mutane suke ciki na dukiya, wannan duk ba shi bane rayuwa na farin ciki. A kullum ka riko rokon Allah SWT ya yarda da kai, kuma Allah SWT ya so ka. Saboda haka abin da ya kamata shi ne mu ji tsoron Allah SWT mu guji saba maSa. Don mun ga mutane da yawan dukiya ko matsayi na mukami ko duk wani daukaka, ko ka ga har wani yana jin dadi yana tare da masu matsayi, ya samu yardar manya; ‘Ai mun yi waya da Alhaji yace yana Landan, daga nan zai wuce Faransa…’ Wani dai shi ko wannan ya ishesa kasaita, sai a ga kamar wadannan mutane sun samu wata Daula ta Duniya, wannan ba ita ce alama ta yardar Allah ba; Allah SWT yana ba da Duniya ga wadanda yake so da kuma wanda ba ya so. Da ace darajar wannan Duniya ta kai na fiffiken sauro a wajen Allah, da kafiri bai samu ruwan da zai kurba ba. Shi yasa ma Malamai ke cewa Allah SAW ya hana Manzon Sa, ba-dadin Sa Duniyar duk da cewa shi ne zababben zababbu wanda ya fi kowa martaba da daraja cikin halittu. Tare da haka Allah ya zabawa Annabi SAW rayuwa ta talauci da kuma yunwa, Allah ya fada maSa cewa: ‘Lahira ta fiye maka wannan Duniya.’ Da Duniya tana da daraja da babu wanda zai fi samun babban rabo irin Annabi SAW kamar yadda Allah mai girma zai fifita Sa SAW a Ranar lahira; Manzon Allah SAW zai kai matsayi na Mukamal-Mahmud wanda babu wanda ya isa ya kai wannan matsayi a Kiyama. Sau da yawa Sahabbai sun ga Manzon Allah SAW ya daura duwatsu a kan cikin sa saboda yunwa, ko da Manzon Allah ya bar Duniya abincin da ya rage a gidan sa kankani ne a cikin wani ‘dan karamin mazubi; wanda dai Allah ya sa masa albarka. Annabi SAW ya rasu ya bar sulken yakin sa a hannun wani Bayahude jingina inda aka ba sa abinci, sai bayan Manzo ya bar Duniya aka karbo wannan sulke na Sa. Idan har da wadata ta isa wani abu, da wa ya fi cancanta da ita? To amma kuma ka da mutane su dauka abin da ake so shine mutum ya zauna ba tare da nema ba. A’a mutum ya nema, amma fa ka rika tunawa da rayuwar Manzon Allah SAW kuma ka godewa Allah, sannan ka yi amfani da abin da ka samu wajen abin da Allah yake so. Yana daga cikin rafkana idan har Allah ya shimfidawa mutum Duniya ya kasance mai sabon Allah. Ka da ya zama kamar Kafirai wanda an gaggauto masu duk wani jin dadin su a cikin wannan Duniya, bai kamata Musulmi ya zama mai irin wannan dabi’ar ba ta maras rabo a Lahira. Manzon Allah SAW ya kira wannan da istidraji, duk wanda Allah yayi wa wannan mugun kamu to ba zai kufce ba. Mutum zai kasance yana ta sabon Allah yayin da yake ta kara samun ni’imar Ubangiji, sannu dai Ubangiji zai damke sa ba-zata. Saboda haka samun ni’imomi ba sa nuna cewa Allah yana son mutum, kai dai ka cigaba da aikata abin da Allah yake so, sai Ya so ka. Yana daga cikin siffofin wadanda Allah ya yarda da su, ka ga bawa ya kaskantar da kan sa ga Ubangiji tare da biyayya da jin tsoron Sa. Yana kuma daga ciki ka samu mutum mai yawan tuba da kuma mu’umala na gari da sauran bayi tare da tsarkaka daga ayyukan assha. Haka kuma yana daga cikin halin wadanda Allah yake so ka ga mutum yana hakuri da juriya wajen biyayya ga Allah da kuma gujewa saba masa tare da hakuri ga abubuwan da su ka same sa yana mai dogaro da Allah SWT shi kadai. Haka kuma wadannan mutane shirye suke da yin gwagwarmaya domin Allah. Sai dai duk wadannan ba su yiwuwa sai mutum yayi riko da sababi. Ba zai yiwu don mutum yayi dogaro da Allah ba kurum ya koma Masallaci yayi ta zikiri ba tare da ya fita ya nemi abinci ba. Dole sai mutum ya nemi ko iri na gona yayi shuka idan an yi ruwa, sai ya dogara da Allah. Dole fa duk abin da za muyi ya zama addini ya yarda da shi kamar yadda Al-Kur’ani ya fada mana; da ace Jama’a za su yi imani su ji tsoron Allah sai Ubangiji ya bude masu hanyoyi na albarkatu ta sama da kasa, sai dai Jama’a da dama suka karyata haka, aka kuma damke su.


Allah ka ba mu fahimtar Addini tare da zama lafiya. Allah ya karba mana ya tseratar da mu daga wuta. Allah Ya Sa albarka cikin aikin mu tare da dadin tsira ga Annabin Mu da Iyalan sa da wadanda suka yi imani da Shi zuwa Ranar karshe.
Allah ka taimaki kasar mu ka taimaki shugabannin mu. Allah ka taimaki mai son gaskiya ka taimake sa ka kuma ba sa lafiya. Ya Allah don kudarar Ka da iradar Ka, Ka ba shugaban Kasar mu lafiya ka maido mana da shi lafiya ya cigaba da abin da yake yi na alheri. Ameen.



Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Muhammadmalumfashi@gmail.com          
Twitter: @Ya_waliyyi


Friday, February 24, 2017

Wani mugun ciwo ya dawo Najeriya



Wani mugun ciwo ya kara dawowa Najeriya



‘Lassa’ mugun cutar nan da aka sani ta dawo gari yanzu haka har ta aika wasu bayin Allah Lahira. Kamar dai yadda aka sani dabbobi irin su bera ne ke kawo zazzabin na Lassa.

Kamar yadda muka samu labari daga jaridar Daily Trust, wannan mugun cuta ta dawo Garin Bauchi har kuma tayi sanadiyar mutuwar mutane 4. Kwamishinar lafiya ta Jihar bauchi Dakta Halima Mukaddas ta bayyanawa manema labarai wannan a yau.

Dakta Halima tace an samu bullowar cutar ne a Garuruwan Alkeri da Ganjuwa. Kwanakin baya dai wannan zazzabi na lassa ya bullo gari inda yayi sanadiyar rashin rayukan mutane kusan 2 a Bauchi. An dai gargadi Jama’a su guji bera wanda shi ke yada kwayar cutar.



[NAIJ Hausa]

Za a samu husufin rana a Najeriya


– Za a samu husufin rana a Najeriya


– Masu nazari sun ce Ranar Lahadi wannan abu zai faru


Sai dai an ce abin ba zai yi kamari ba




Masana masu hange da binciken Duniya sun bayyana cewa za a samu husufin rana a sassan kasar nan a Ranar Lahadi. Ko da yake dai masanan sun ce abin ba wani mai kamarin gaske bane.

Kungiyar bincike game da cigaban sararai na kasa watau NASRDA tace wannan abu zai faru ne karshen makon nan kamar yadda ta fadawa hukumar dillacin labarai na kasa NAN jiya a Birnin Abuja.

Masanan sun ce wannan abu zai faru ne a ko ina na fadin kasar. Hasken ranar za ta fi raguwa ne kuma a Yankin kudancin kasar irin su Fatakwal, Kalaba da Garin Uyo. Inda kuma abin ba zai yi wani tasiri ba shi ne Yankin Arewacin kasar musamman Jihar Kebbi.

Wannan abu dai zai faru ne da yammaci akasari daga bayan karfe 4 zuwa karfe 6. Ba dai yau aka fara samun husufi a Najeriya ba, kuma baa bin tada hankali bane. A irin wannan yanayi mutane kan fito suyi ta addu’a.


[NAIJ Hausa]


Osinbajo zai gyara tattalin arzikin Najeriya a wata 2





Mukaddashin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya shirya farfado da tattalin arzikin Najeriya cikin watanni biyu. Najeriyar dai ta samu durkushewar tattalin arziki a a bara.


Farfesa Osinbajo ya kulla niyyar shawo kan matsalar tattalin arzikin Najeriya cikin kankanin lokaci. Shugaban rikon kwaryar dai zai cin ma wannan burin ne ta hanyar saukake harkar kasuwanci a kasar.

Yanzu haka an nada wani kwamiti wanda shi mukaddashin shugaban kasar yake jagoranta mai suna PEBEC wanda zai kawo sa’ida wajen harkar kasuwanci a Najeriya. Hakan zai taimakawa kananan ‘yan kasuwa na kasar ya kuma habaka tattalin arziki cikin kwanaki 60. Ana so dai duk wani dan kasuwa da zai zo Najeriya da hajar sa ya kammala kamai cikin ‘yan sa’o’i.

Jiya ne shugaban rikon kwaryar ya dura filin jirgin saman Legas ba tare da tsammani ba inda ya rika bincika abubuwa da kan sa. Gwamnati na kokarin ganin Najeriya ta shiga sahun kasar da kasuwanci ya ke da sauki ba tare da wahala ba, wannan zai taimakawa tattalin arzikin kasar.



[NAIJ Hausa]

Ayyiriri: Naira tayi sama


– Naira tayi tashin da ba ta taba yin irin sa ba


– A cikin ‘yan kwanakin nan dai Naira tana kara mikewa




Da alamu hakar babban bankin Najeriya na CBN za ta ci wa ruwa don kuwa har abubuwa sun fara yin kyau. Kwanan nan ne dai babban bankin kasar watau CBN ya sauya tsare-tsaren sa na harkar kudin kasar.

Makon jiya dai sai da Nairar tayi irin dukan kasar da ba ta taba yi ba, don kuwa an wayi gari an samu Dalar Amurka tana kan Naira 520, Tun da ake ba a taba samun lokacin da Naira ta fadi war-was kamar haka ba.

Yanzu haka dai ana sayar da Dalar Amurka a kan N470 wanda an samu ragin kusan N50 kenan cikin ‘yan kwanaki biyu. Babu dai lokacin da Naira tayi irin wannan yunkuri. Kwanan nan ne babban bankin kasar watau CBN ya saki dalolin miliyoyi ga bankuna, hakan ya kawo sa’ida wajen samun dalar.


A wani bangaren kuma, Farfesa Osinbajo ya aikawa Sufeta-Janar na ‘Yan Sanda Ibrahim K. Idris kira game da yawan satar mutane da ake samu a Najeriya. Kwanan nan ne aka sace wasu turawa ‘Yan kasar Jamus 2 a cikin Jihar Kaduna. 


[NAIJ Hausa]

An sallami Ranieri daga Leicester City



Kungiyar Leicester ta raba jiha da Kocin ta Claudio Ranieri


– Ranieri ya ci wa Leicester Kofin Firimiya a bara


– Sai dai bana abubuwa sun sukurkucewa Leicester bana



A shekarar bara ne dai Kungiyar Leicester City ta Ingila tayi abin da kusan ba a taba yi ba a Duniya. Leicester City ta lashe Gasar Firimiya na Ingila ta maki kusan 10, wanda babu wanda ya taba kawo haka a ran sa.

A shekarar nan ne Hukumar FIFA ta ba Kocin na Leicester City kyauta a matsayin gwani-na-gwanaye cikin masu horaswa. Sai dai ga shi bayan wata guda an tsige Kocin bayan Kungiyar ta gaza tabuka wani abin kirki wannan shekarar.




Kusan dai shekaru 4 da suka wuce duk Kocin da ya ci kofin Firimiya sai da ya bar Kulob din sa, fara daga Kocin Mancehester City Roberto Mancini, da na Manchester United Sir Alex Ferguson. Ga kuma Manuel Pellegrini na Man City, haka kuma Jose Mourinho ya bar Chelsea bara bayan ya ci Firimiyar wancan shekarar.

Wasu dai na ganin bai dace a sallami Claudio Ranieri ba komai ya faru, don kuwa a zaman Kulob din na shekaru 100 babu wanda ya taba irin kokarin sa. Sai dai kuma fa Kungiyar na cikin hadari babba. Manyan ‘Yan wasan ta Riyadh Mehraz da Jamie Vardy duk sun yi sanyi.



[NAIJ Hausa]

Thursday, February 23, 2017

Mufti Menk ya goyi bayan Sarkin Kano


– Babban Malamin Duniya Mufti Menk ya goyi bayan Sarki Sanusi II


– Sarkin Kano yace za a hana talaka yawan aure a kasar sa


Malamin yace Sarkin Kano yayi daidai kuma ‘Yan Jarida ba su kyautawa




Babban malamin Duniya mai fatawa Sheikh Ismail Menk ya goyi bayan Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II a game da maganar cewa za a hana talaka tubus kara auren mata a kasar sa. Kalamai da kudirin na Sarkin Kano sun jawo ce-ce-ku-ce a Gari.

Mufti Menk ya nuna goyon bayan sa ga yunkurin Sarkin yace dama can aikin Hukuma ne ta duba yadda ake gudanar da al’umarra ta kuma kawo gyara. Malamin yace ‘Yan Jarida ne ke kara hura wutar maganar inda suke nuna cewa Sarkin na nema yayi fada da Sunnar Manzon Allah SAW.




Babban Shehin na kasar Zimbabwe yace ko da cewa aure Sunnah ne mai karfi, amma ko Manzon Allah SAW cewa yayi wanda yake da hali yayi, wanda kuma ba sa da shi sai ya hakura, ina kuma maganar karawa.

Malamin yace hakan zai kawo gyara a harkar aure inda za a mutunta darajar ‘ya ‘ya da kuma mata. A wata hira da Hukumar dillacin labarai na kasa watau NAN tayi da wasu mata a Maiduguri, wasu sun bayyana cewa hakan abu ne mai kyau yayin da wasu suka yi tir da batun.


[NAIJ Hausa]

Buhari yayi magana da mutanen Kano


– Manyan malaman Kano sun yi shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’a


– Sheikh Daurawa yace shugaba Buhari na bukatar addu’a


Gwamna Ganduje yayi magana da shugaba Buhari





Kusan duk wani babban malami yana cikin gidan gwamnatin Jihar Kano jiya inda aka yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’a. Malaman sun yi wa shugaban addu’ar karin lafiya ya samu ya cigaba da mulkin kasar nan.

Manyan malami irin su Malam Aminu Daurawa, Sheikh Isiyaka Rabi’u, Sheikh Muhammad Nasir Adam, Sheikh Adam Suleiman da sauran Shehunnai suka halarci gangamin inji Jaridar Vanguard. An dai ta karatun Kur’ani domin shugaba Buhari ya samu waraka.

Shugaban Hisbah Sheikh Daurawa yace shugaban kasar na bukatar lafiya domin ya cigaba da tafiyar da al’amurar kasar nan tare da goyon bayan Jama’a. Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi magana kai-tsaye da shugaban kasar inda ya bayyana yadda Jama'a ke ta masa addu'a, shugaba Buhari yayi matukar godiya ga mutanen a wayar tarho.





[NAIJ Hausa]






Wednesday, February 22, 2017

‘Yan Najeriya sun yi ca a kan Sarkin Kano


– Mutane sun fara tofa albarkacin bakin su game da maganganun Sarki Sanusi II


– Sarkin Kano yace za a hana talaka yawan aure a kasar sa


Wannan maganar ta jawo ce-ce-ku-ce a Gari




Kalamai da kudirin Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II sun jawo ce-ce-ku-ce a Gari yanzu haka a cikin mata. Mai Martaba Muhammadu Sanusi II yace za a hana talaka tubus kara auren mata a kasar sa.

A wata hira da Hukumar dillacin labarai na kasa watau NAN tayi da wasu mata a Maiduguri, wasu sun bayyana cewa hakan abu ne mai kyau yayin da wasu matan kuma suka ce gaba daya bai dace a kawo irin wannan doka ba. 

A wani bincike da Jaridar Daily Trust tayi wasu matan sun nuna cewa sun yi na’am da Sarki suka nemi kuma a mara masa baya, wasu matan dai sun ce hakan na iya kawo matsala ga matan da ke neman mazaje ido rufe.

Sarkin dai yace za a hana wadanda talauci ya masu katutu aure barkatai wanda a karshe suke gaza kula da ‘ya ‘yan su, Sarkin yace wannan ke kawo ‘ya ‘ya a Gari wadanda suke zama ciwon kai ga al’umma. Wasu dai sun ce ko ya za iya da tarin ‘yan matan da ke Gari?



[NAIJ Hausa]

'Yan Najeriya sun ga azaba a kasar waje

– Mutanen Najeriya da suka dawo daga kasar Libya sun ce ba irin wahalar da ba su gani ba a can


Jiya aka dawo da wasu ‘yan kasar nan daga Libiya


– ‘Yan Najeriya sun bayyana irin hazan da su ka ji a kasar waje





A jiya Talata ne jirgi ya sauka daga kasar Libiya dauke da ‘Yan Najeriya a filin jirgi na Murtala Muhammad da ke Legas. ‘Yan Najeriyan dai sun bayyana irin yadda suka samu rayuwa a inda suka je, suka ce babu irin bala’in da ba su gani ba.

‘Yan Najeriyan sun ce sun ga azaba a kasar Libiya, suka ce asali ma dai yaudarar su aka yi su ka tafi kasar tun farko, yanzu haka dai wadansu mutane 171 daga cikin mutanen sun ji ba Sarki sai Allah sun tsero Inji Hukumar Dillacin labarai na kasa watau NAN.




Wata mata mai suna Gift Peters tace ita dai yaudarar ta aka yi, aka ce mata za a kai ta kasar Italiya, sai ga su sun buge a kasar Libya da ke Arewacin Afrika. Wannan mata tana hawaye tace har bawali sun sham wani lokaci kuma a nana masu karfe mai zafi saboda azaba.

Mutanen dai sun yi da na-sani suka komai lalacewa gida ya fi daji. Shugaban kasa dai yayi alkawarin za a taimaka ma wadanda aka dauka daga kasashen. 


[NAIJ Hausa]

Rashin wutan lantarki ke hana mu aiki-Minista


– Ministan harkokin mata tace sai su fi makonni 5 ba tare da wutan lantarki ba


– Aisha Jummai Alhassan ta bayyana haka ne a gaban majalisa


Rashin wuta dai ya zama ruwan dare a Najeriya





Da alamu dai rashin wutan lantarki ya zama ruwan-dare a Najeriya, a jiya ne Ministar harkokin mata Aisha Jummai Alhassan tace har Ma’aikatar ta sai a shafe fiye da wata day aba tare da kiftawar wuta ba.

Mama Taraba kamar yadda aka san ta, tace rashin wuta ne ya hana ta kawo takardun da ake bukata wajen tattaunawa da kuma tsefe kasafin ma’aikatar na wannan shekarar. Aisha Alhassan tace rashin wuta ne ya addabe su a Ma’aikatar wanda a wani lokaci sai a kusa makonni 6 babu wutar lantarki.

Ministar tace dole ita da Sakataren Ma’aikatar suka hada kudi daga aljihun su suka saye man da aka yi amfani da shi a Injin janareto. Ministar tace rashin wuta ne dai ya hana ta zuwa ta kare kasafin ma’aikatar ta a Majalisa, tace ba za a kara yin hakan ba. 

Haka dai kwanaki aka dauke wuta yayin da ake tantance Jakadun kasar a cikin Majalisar Dattawan Kasar. Rashin wuta dai ya zama ruwan-dare.


[NAIJ Hausa]







Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...