Friday, March 31, 2017

Cutar sankarau ta shigo Jihohin Arewa


 Sankarau na cigaba da kashe mutane a Arewacin Najeriya




Cutar sankarau na cigaba da yaduwa a Jihohin Arewa inda da dama su ke mutuwa a dalilin haka. Cutar yanzu ta uka Garin Sokoto, Bauchi, Katsina da ma wasu Garuruwan.

Ma’aikatar lafiya ta Gwamnatin Jihar Jigawa ta bayyana cewa cutar sankarau ta hallaka mutum guda yayin da wasu kuma su ka kara kamuwa da cutar kamar yadda NAIJ.com ke samun labarin a halin yanzu.

Dr. Muhammad Kainuwa Darekta ne a ma’aikatar lafiya ya bayyana cewa cutar ta kashe wani karamin yaro a Garin Gwaram. Haka kuma dai an samu yaduwa cutar a Garuruwan Kiaywa, Gwaram, Maigatari da Kirikasamma.

Babbar matsalar da ake fuskanta dai it ace rashin magunguna a Yankin, Dr. Kainuwa yake cewa da zarar an samu magani za a ci karfin wannan mugun cuta wanda ta fara addabar Yankin arewa musamman Sokoto, Bauchi da sauran su.

A Jihar Sokoto Kwamishinan ya bayyana cewa an samu aukuwar cututtuka fiye da sau 330 a Kananan Hukumomi 7. A ciki dai an samu wasu da su ka bakunci lahira don yanzu haka dai annobar na ta kara kamari inda ta ga bayan mutane akalla 21 a Garin.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...