Shugaba Buhari yayi magana
A jiya ne muka samu labarin
cewa shugaban kasan Najeriya Muhammadu Buhari zai dawo gida Yau Jumu’a. Shugaba
Muhammadu Buhari dai ya dauki kusan kwanaki 50 a Landan
A yau ne shugaba Muhammadu Buhari ya dawo Najeriya da
asuba. Shugaban kasar ya iso filin jirgin sama na Kaduna a Jirgin shugaban kasa
na Air force kimanin karfe 4:00 na safiya. Mataimakin Gwamnan Jihar Bala Bentex
suka tarbe sa.
Bayan nan ne shugaban kasan ya karasa Birnin Tarayya
Abuja a wani dan karamin jirgi, A nan dai Mukaddashin shugaban kasa da sauran
kusoshin Gwamnati wanda sun dade suna jiran sa. An ga Farfesa Osinbajo da mai ba
shugaban kasa shawara game da harkar tsaro Manjo-Janar Munguno suna ta
tattaunawa.
Bayan lokaci kadan sai ga jirgin shugaban kasar nan ya
dura, Jami’ai kuma suka zagaye say a fito. Shugaba Buhari ya fara gaisawa da
Mataimakin sa Farfesa Osinnajo sannan ya gaisa da Abba Kyari da kuma Gwamnan
Zamfara da Ministan Abuja, sannan ya gaisa da sauran manyan Jami’ai.
Shugaba Buhari ya gaisa da Femi Adesina kenan sai wani
Dan Jarida ya tambaye sa ko ya jikin sa. Shugaba Buhari ya fada masa cewa ai ga
shi nan yana ganin sa. Nan shugaban kasar ya shiga motar sa ta Marsandi S550
zuwa Fadar Aso Rock.
No comments:
Post a Comment