HUDUBAR JUMA’A DAGA
MIMBARIN ITN-ZARIA
Dawowar Shugaba Buhari-Daga Bakin Imam Dr. Saeed Muhammad Yunus
Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah,
Dukkan Godiya sun tabbata ga Allah SWT mai ni’ima mai falala wanda ke daga
wanda ya so ya kuma sauke wanda ya so. Muna shaidawa bai da ‘da ko mata ko
tamka ko wani abokin tarayya. Mun kuma shaida shi ya aiko Annabi Muhammad SAW a
matsayin Shugaba. Muna gode masa da gaisuwa gare sa.
Bayan haka:
‘Yan uwa mu ji tsoron Allah mu kuma gode masa, muyi da’a gare sa mu kuma
nisanci munanan ayyuka. Mu sanya katanga ko ginshiki da zai kare mu daga azabar
Allah. Mu godewa Allah da ya saka mana ni’ima ta Musulunci da lafiya da kuma ni’imar
ganin ayoyi; daga ciki mun ga cewa Allah SWT shi ke dagawa kuma shi ke saukeawa.
Allah SWT shi ke gudanar da rayukan dabbobi har da kwari. Saboda haka in dai ni’ima
ce ba za mu iya kididdige yawan su ba kamar yadda Allah SWT ya fada mana.
Wata Juma’a ce sabuwa ga ‘Yan Najeriya wanda ta cacanci ayi mata huduba ta
musamman saboda Allah SWT ya dawo mana da wani wanda muke so-wanda Allah ne ya
sa mana son sa. Na rantse da Allah ba shi bane ya sa mana son sa, Allah ne ya
sa mana son na shi. Don Allah yace da Manzon Allah cewa: ‘Allah ne ya karfafe
ka da nasara ya kuma hada ka Muminai wanda suke taimakon ka… Amma yanzu idan da
za ka ciyar da duk abin da ke Duniya, ba za a so ka ba.’ Yanzu idan ka isa ka
taba mutuncin Manzon Allah SWT sai ka ga mutane wadanda ba su san Manzon Allah ba
ko ya za suyi maka. Haka ne Allah SWT ya sakawa Jama’a son Muhammadu Buhari a
Najeriya. Wannan ko kana so, ko kana ki sai dai kayi hakuri kurum, don haka Allah yake
zaben bawa daga cikin bayin Sa yace a so shi. Ubangiji ne ya sa Jama’a ke kaunar
Muhammadu Buhari ba ko kudi ya ba mutane ba, wani yana rike da kudi fiye da na sa. Wani yana da dangantaka
wanda ta fi tasa. Kai wani ya kasance yana da iko da makamai a lokacin da shi
Buhari ba shi da su, amma Allah SWT ya daga sa.
Saboda haka ‘Yan uwa mu natsu! Mu lura da ayoyi na Allah. Ubangiji ya fada mana cewa Allah
zai ta nuna maku ayoyi ya ga ko a wane za ku yi musu. Allah SWT yana cewa za mu
yi ta nuna masu ayoyi a nan da can har ga ma kawunan su. ‘Yan uwa kasa ta cika
da zalunci da kama-karya irin na zamanin jahiliyya da Manzon Allah SAW ya gada;
an tsiri Manzon Allah SAW ne a lokacin da ake shan giya ake cin naman alade,
ana kashe mata ana karbe dukiyar Jama’a. Sai ga Annabi SAW kuma har bayan Manzon Allah
aka yi ta samun Halifofin sa da wanda su ka biyo baya.
Jama’a idan muka duba abin da ya rika faruwa a Najeriya za mu ga yadda
tarbiyya ta lalace; babu babba babu yaro. Ga Sarakuna iyayen kasa da manyan
Malamai a Garuruwa, duk sun zama ba su da wani daraja ko kadan. Kasar mu ta
kasance mun zama ba mu da tsari ko sahu. Kasar nan ta zama cewa komai yadda ka
rufe kofar gidan ka wani na iya fado maka cikin dare yayi maka barna. Mun wayi gari a wannan kasar wasu za su
tare ka suyi maka fashi ko wani ya banke ka ya tsere. Wannan fa abin da yake
waje kenan, idan ka shiga cikin gidaje za ka ga yadda ake zaluntar iyaye mata
da su ma yadda suke zaluntar mazajen su ta hanyoyi da dama. Ka leka Ofisoshi za
ka ga yadda Ma’aikatan Gwamnati suka zama manyan barayi sannan kuma ga wasu da
ake kira ‘Malamai’ da suke yi masu fatawa cewa su diba kudin ba komai ga hakan
ko da cewa akwai hadisin Manzon Allah SWT da ke cewa: Wadansu mutane suna kutsawa
cikin dukiyar Allah mai girma ba tare da hakkin su ba, Ubangiji SWT kuma yana kallon su, Manzon Allah yace
wadannan mutane a ranar lahira ‘yan wuta ne. Dukiyar Najeriya ta kasance na
wasu mutane ne da suke rabawa tsakanin su. Ina rantse maku da Allah babu wanda ya
tsira daga wannan; har ta kai wani yana izgili yana fada cewa duk wanda ya fito
masa da rana sai yayi shanya!
Wannan abin bakin ciki ne da aka dade ana yi a Najeriya kwatsam sai ga wata
rana da aka yi zabe a Najeriya, a wannan karo kuri’a tayi tasiri yayin da
talakawa su ka yi zabe. Tun da dai an yarda da wannan tsari na Damukaradiyya
wanda Musulunci yace ayi tayi muddin ba za a hana Musulmi ibadar sa ba. Sai ga Allah SWT ya daga wani wai shi
Muhammadu Buhari a Najeriya. Amma abin da zai ba ka mamaki shi ne akwai Makiya
ciki da waje, masu kin wannan gyara da ake so ayi domin Jama’a su samu aminci. A zamanuin
Sarki Umaru dan Abdulazeez ya kasance sai kere-keci ta hadu da akuya tayi mata
sallama, haka ake fata cewa a sa mu dawwama kowa kuma ya ji dadi! Abin ban sha’awa
dai Addinin musulunci bai hana Shugaba ya taimakawa wanda ba Musulmi ba, mu
duba yadda Annabi SAW yayi mu’umala da Yahudawa har wasu suka musulunta. Dama
dai ba fatan mu kowa ya musulunta ba don kuwa an fadawa Annabi SAW sau da dama a
Kur’ani cewa: Za ka tilastawa mutane su zama musulmi? Ba za ka iya ba…’
Ubangiji bai daurawa Jama’a wannan ba. Lalata ta shiga har cikin Malamai masu ‘taimako’
wanda da su ake yin wannan badakalar. Akwai mata mazinata da mashaya giya mai
tsada, sace-sace da barna sun cika Kasar nan. Abin bakin ciki sai dai wasu abin
da suke so shi ne a cigaba da wannan aiki. Ku duba fa ko an yi maganar gyara a
yanzu sai kace har yanzu kadan aka gyara don kuwa an tauna tsakuwa ne sai aya
ta firgita. Idan har muna da hankali za mu iya tuna abubuwa da suka faru baya.
Wata sabuwar Juma’a ce ga ‘Yan Najeriya da Allah mai girma ya nunawa aya.
Saboda haka ‘yan uwa ku ji tsoron Allah cikin maganganun ku sannan ku kiyayi
Allah SWT. Wasu maganganun ku da kare-karen za su zame maku bala’i a Ranar Lahira. Wallahi za ku
shiga uku a gobe kiyama!
‘Yan uwa ku tuna abin da ya faru a baya Inji Huduba, mu tuna abin da ya
faru a baya; ya kasance fitowa daga Sabon Gari ko cikin Zariya zuwa Jami’ar
Ahmadu Bello da ke Samaru ya zama tashin hankali, kullum sai an yi wa iyali wasiyya. Idan
kuma har ka je inda abin yake faruwa, to babu yaro kuma babu babba. Mutane suna
cikin damuwa babu mai taimako; an kama samari an yanka kamar rago, kananan yara
kuma an kashe su kamar kiyashi, ba a tausayin tsoho idan ya nemi ya wuce gona
da iri. Daga ana kokarin zuba ruwa sai ka ga wata wutar fitinar ta taso. Har
aka samu wannan yanayi, Idan ba ka sani ba, ka nemi a ba ka labari.
‘Yan uwa huduba tana ce mana ina wadanda suka ce Ai Buhari ba zai dawo ba?
To Allah ya dawo da shi. Al-Kur’ani ya fada mana yadda wasu suka yi alkwari
cewa za su yi imani idan har wata ya tsage kuma bayan wata ya tsage kamar yadda
su ka nema, sai kuma ba su yi imani ba. Haka mutanen Annabi Salihu AS suka nemi
Allah SWT ya fito da Taguwa daga kurman dutse, Annabi Salihu ya roki Allah kuma
taguwar ta fito, amma sai su ka soke ta! To ku ‘Yan Najeriya da ku ka ce za ku
musulunta idan har Buhari ya dawo, to muna jiran ku da musulunta, idan akwai
wasu a cikin wannnan masallaci sai
ku zo ku karba Musulunci, ga ni ina nan kan mimbari, idan kuma kuna jin kunya sai ku tafi
masallacin Unguwa ku musulunta.
Allah ya cika alkawarin sa! Malamai za su fada maku cewa Allah Mai Girma ba
ya son wuce gona da iri; wani ya bugi kirji yace sai abu kaza ya faru da wane. Wani ya taba cewa
ga wani zai shiga wuta, sai Allah SWT ya aika masa cewa ya yafewa wancan, kuma
shi ne zai shiga wuta. Duk matsayin ka da Allah ba ka isa ka ce da wani ba zai
shiryu ba; Dubi yadda Manzon
Allah ya rika ambaton wadanda suka kashe masa Sahabai a Sallah yana tsine masu,
sai Allah SWT ya saukar da aya a Al-kur’ani.
Jama’a menene abin gaggawa idan har wannan Dattijo ya rasu? Manzon Allah
Muhammadu SAW ya cika, Allah ya fadawa al’umma cewa idan har Annabi ya bar
Duniya shin za ku bar Addini? Shin daga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya rasu
kuma sai a bar gyara a Najeriya? Ai kuwa da mun shiga uku idan har babu wani
irin sa mai gyara a Najeriya. Idan har mu Musulmai ne na kwarai sai mu fara
gyara halayen mu, mu nemi tarihin Buhari tun kafin ya rasu.
Ni dai na ga lokacin da shugaban kasa ya sauko daga jirgi ya kuma zarce
Abuja. Ina maku haduba cewa ga sako nan na wuce gona da iri da wasu ke yi. An matsu a wancan lokacin Manzon Allah SAW ya rasu, Allah Mai Girma yace idan har
Annabi SAW ya rassu shin su za su dawwama ne?
Duk mai rai mamaci ne. Wata rana Sayyidina Umar RA yayi huduba yace kowa ya
shiryawa mutuwa. Can wata rana kuma dan sa Abdullahi dan Umar RA sai yace dukkan mu nan matattu ne! Don haka ina kara
fada cewa dukkan mu nan matattu ne. Wasu daga cikin wadanda su ke wannan magana
yanzu sun riga Shugaban kasar rasuwa. An ce dama mutuwa gida ne da kowa sai ya
shiga don haka huduba na fada mana cewa mu yi hankali da bakunan mu domin za
ayi mummunar azaba ga harshe a gobe kiyama. Annabi SAW ya fadawa Sahabi Abu
Hurayrah AS ya kiyaye harshen sa. Haka kuma Jama’a su guji wuce gona da iri
wajen murna kar mu zama kamar Mahaukata. Mu roki Allah ya taimaki kasar nan da ‘Yan
Jam’iyyar Buhari da wadanda ba su ba.
Allah ya taimake mu ya karawa Buhari lafiya ya sa ya
zama tsani domin gyaran Kasar nan. Allah duk wani mai kunci ka yaye mas aka azurta
Buhari da Mashawarta ka kare sa daga Munafukai. Allah ka shiryar da lalatattu
kar ka sa mu lalace. Ameen.
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga
Masallacin I.T.N-Zaria.
Twitter: @Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment