Thursday, March 2, 2017

Su wa ke nema a hana ‘Achaba’



– Ministan sufuri yace bai dace Gwamnoni suyi kokarin hana Achaba ba


Rotimi Amaechi yace hana ‘Achaba’ zai kawo babbar matsala a Najeriya


– Gwamnoni dai na kokarin hana hawa babur da keke napep



Ministan sufuri na kasa Rotimi Amaechi yace bai dace Gwamnoni suyi kokarin hana Achaba ba. Amaechi yace hakan zai kawo matsala ne kurum ga tattalin arzikin kasar don haka ya gargadi Gwamnonin kasar da wannan kudiri.

Rotimi Amaechi ya bayyana haka ne ga hukumar dillacin labarai watau NAN wajen taron kungiyar masu ‘keke napep’ da babur na kasa. Amaechi yayi wa Gwamnoni kashedi cewa kul aka hana Jama’a hawa achaba domin zai kara radadin da ake ciki na tattalin arziki.

Ministan yace abin da ya kamata ayi shi ne a koyawa ‘yan achaban da sauran matuka aiki da bin dokar hanya saboda irin yawan haduran da ake samu a a fadin kasar. Amaechi yace masu babur suna da amfani don kuwa ba ko ina mota ke iya ratsawa ba.



[NAIJ Hausa] 





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...