Monday, March 20, 2017

Da gaske Dino Melaye bai gama A.B.U ba?


Ashe wani babban Sanata bai kammala makaranta ba?




Jaridar Sahara Reporters ta tasa wani Sanata a gaba inda tace ashe bai kammala Jami’ar ba. Sai dai Sanatan ya maida martani yace ayi a gaji a kyale sa

Jaridar Sahara Reporters ta bayyana cewa Sanata Dino Melaye bai karasa karatu a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya ba aka sallame sa. Sahara Reporters ta fitar da hotunan kwas-kwasan da Sanatan ya dauka inda aka nuna cewa ya fadi.

Sanatan ya mayar da martani inda yace sharri ne kurum ake masa. Melaye yace nan gaba ma ana iya cewa shi ba ‘Dan Najeriya bane. Sanata Melaye yace ba wannan bane karo na farko da Sahara Reporters tayi masa sharri.

Dino Melaye ya bayyana cewa yanzu haka yana karatu a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariyar inda yake Digirin sa na 7. Sanatan yace a je a duba idan har karya ne a sa Magu na EFCC ya kama sa ya daure.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...