Wednesday, March 8, 2017

Yadda muka rike Najeriya-Gowon







Kwanaki aka yi ta faman yada cewa tsohon shugaban kasa Yakubu Gowon ya samu cikawa. Ga dai Yakubu Gowon din ya fito da kan sa inda ya bada labarin yadda suka rike Najeriya a baya.

Tsohon shugaban kasa Janar Yakubu Gowon ya bayyana yadda Marigayi Obafemi Awolowo ya hana Najeriya wargajewa a lokacin yakin basasa na Biyafara. Gowon ya bayyana haka ne a Ranar tunawa da Marigayi Awolowo. 




Yakubu Gowon yace a lokacin Cif Obafemi Awolowo yana Minista, Najeriya ba ta karbi aron kudin ko sisi ba har aka kammala wannan yaki na basasa. Gowon yace Marigayi Awolowo da sauran wadanda ke gwamnati suka ba sa shawarar yadda za a tafiyar da gwamnati.

A taron dai Gawon yace bai taba furta cewa kasar Najeriya tana da kudi har ta rasa abin da za tayi da su ba a lokacin yana shugabanci. An dai dade ana yawo da wannan maganar da sunan tsohon shugaba Yakubu Gowon din.

Gowon yace idan da su Awolowo za su tashi daga kabari ba za su ji dadin ganin yadda Najeriya ta zama ba. Kwanan nan shugaba Buhari ya kira Yakubu Gowon din inda yayi masa ta’aziyar rasuwar kanwar sa Martha Kande Audu wanda ta cika kwanakin baya.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...