Sunday, March 5, 2017

Ana cigaba da budawa Kocin Arsenal wuta


Kocin Kungiyar Arsenal Arsene Wenger na kara gamuwa da cikas musamman daga magoya bayan Kungiyar ta Arsenal bayan ya kara shan kashi a karshen wannan makon.




Magoya bayan Kungiyar Arsenal da dama sun fara kiran dole fa Koci Arsene Wenger ya tattara ya san nayi. Masu goyon bayan Kungiyar sun ce tabbas sun gaji da Wenger don haka ya dace kurum ya bar Kulob din.

A jiya ne Arsenal ta sha mugun kashi hannun Kungiyar Liverpool da ci 3-1, wanda wannan dai na iya kawo masu cikas a kakar wannan shekarar. Magoya bayan Arsenal suka ce duk laifin Arsene Wenger ne ya ja aka lallasa Kulob din haka har gida da waje.

A wasan dai Wenger ya ajiye babban dan wasa Alexis Sanchez a benci inda ake tunanin saboda wata takaddama da suka samu ne a wasan su da Bayern Munich makonnin baya. Dan wasa Mane na Liverpool dai ya koyawa Arsenal din hankali.

Dama can Kocin Kungiyar Arsenal watau Arsene Wenger na fuskantar barazana tun bayan da Kungiyar sa ta kwashi kashin ta a hannun Bayern Munich. Kungiyar Bayern Munich din dai ta koyawa Arsenal darasi da ci 5-1 a Gasar Champions League. Har an fara tunanin cewa Kocin Juventus Massimiliano Allegri zai karbe wurin Wenger.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...