Thursday, March 30, 2017

Miliyoyin Jama’a na fama da karancin ruwan sha

Boko Haram: Miliyoyin Jama’a na fama da rashin ruwan sha


A dalilin rikicin Boko Haram Miliyoyin Jama’a na fama da rashin ruwan da za su sha a Yankin Arewa maso gabas kamar yadda NAIJ.com ta samu labari




A wani nazari da aka yi an gano cewa kusan mutane miliyan 4 ke fama cikin rashin ruwa a yankin da Boko Haram su ka yi ta’adi. Boko Haram dai sun barnata kashi 75% na hanyoyin ruwa a Yankin na Arewa maso gabas.

Rikicin Boko Haram dai ya bar dinbin miliyoyin Jama’a babu ruwan sha Inji Kungiyar UNICEF. Kungiyar mai kula da kananan yara tace a Jihar Borno ‘Yan Boko Haram sun gama bata duk wasu hanyoyin samun ruwan sha a Garin.

Karancin ruwan sha da kazanta da rashin lafiya na nema ya zama wani karin tashin hankali a Yankin kasar kamar dai yadda yake faruwa a kasashen Somaliya, Yemen da kuma Kudancin Sudan Inji UNICEF.

Karancin ruwan sha mai tsabta dai na haifar da cututtuka da dama musamman ga yaro karami. Boko Haram dai ba karamar barna su ka yi musamman a Yankin ba inda aka kashe miliyoyi yayin da wasu kuma su ka tsere.

Kwamishinan lafiya na Jihar Sokoto Dr. Balarabe Kakale ya bayyana cewa cutar sankarau kuma na cigaba da kashe mutane a Jihar Sokoto. Yanzu haka dai annobar na ta kara kamari inda ta ga bayan mutane 21.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...