Monday, March 27, 2017

Wani Lauya ya maka Israila kara a Kotu saboda kashe ‘Jesus’



- Wani Lauya a kasar Kenya ya maka mutanen kasar Israila kara a Kotu


- Lauyan yace mutanen Isra’ila ne su ka kashe Yesu Almasihu


- Wannan abu dai ya ba mutane mamaki





Wani Lauya mai suna Dola Indidis a kasar Kenya ya maka kasar Isra’ila a babban Kotun Duniya da ke Birnin Hague kara inda yake zargin mutanen kasar da kashe Yesu Almasihu wanda Musulmai su ke kira Annabi Isa kuma Kiristoci su ke bauta masa.

Lauyan yace kashe Annabi Isa da aka yi a bisa kan sarka ba daidai bane, zallar zalunci ne wanda ya saba hakkin bil adama. Babban Lauyan ya nemi a hukunta kasar Israila da kuma Sarkin Daular Rumawa a wannan lokaci da ma kasar Italiya.

Sarakunan Daular Rumawa ne dai su ka yanke hukuncin kashe Yesu wanda ake kira Jesus a wancan lokaci. Wannan babban Lauya na kasar Kenya yace dole a sake binciken shari’ar da aka yi don kuwa ba a bi ka’idar kotu ba.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...