- Wani Lauya a kasar Kenya ya maka mutanen
kasar Israila kara a Kotu
- Lauyan yace mutanen Isra’ila ne su ka kashe
Yesu Almasihu
- Wannan abu dai ya ba mutane mamaki
Wani Lauya mai suna Dola Indidis a kasar Kenya ya maka kasar
Isra’ila a babban Kotun Duniya da ke Birnin Hague kara inda yake zargin mutanen
kasar da kashe Yesu Almasihu wanda Musulmai su ke kira Annabi Isa kuma
Kiristoci su ke bauta masa.
Lauyan yace kashe Annabi Isa da aka yi a bisa kan sarka ba
daidai bane, zallar zalunci ne wanda ya saba hakkin bil adama. Babban Lauyan ya
nemi a hukunta kasar Israila da kuma Sarkin Daular Rumawa a wannan lokaci da ma
kasar Italiya.
Sarakunan Daular Rumawa ne dai su ka yanke hukuncin kashe
Yesu wanda ake kira Jesus a wancan lokaci. Wannan babban Lauya na kasar Kenya
yace dole a sake binciken shari’ar da aka yi don kuwa ba a bi ka’idar kotu ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment