Tuesday, March 7, 2017

Shin za a gamu da yunwa a Najeriya?



Ministan gona yace babu yunwa a kasar nan ko kusa


Ministan harkar gona da raya karkara Audu Ogbeh yayi wuf ya karyata rahotannin kungiyoyin Duniya da kafafen da ke rahoto cewa akwai matsinaciyar yunwa. Audu Ogbeh yace sam ba haka abin yake ba.

Ministan gona Audu Ogbeh ya karyata bayanan manyan Kungiyoyoin Duniya har 3 da suka bayyana cewa an kamo hanyar shiga yunwa a Najeriya. Kungiyar FAO da WFP da kuma IFAD duk na abinci sun ce Najeriya za ta shiga cikin matsinaciyar yunwa.





Audu Ogbeh ya karyata wannan bincike inda yake cewa hakan ba zai taba yiwuwa ba don kuwa Najeriya ke ciyar da har sauran kasashen Afrika ba kan ta kadai ba. Minista Audu Ogbeh yace babu wannan maganar ko kusa.

Ministan yace Kungiyoyin na cakuda yanayin da ake ciki a bangaren Arewa maso gabas da Boko Haram suka yi barna a matsayin Najeriya gaba daya. Audu Ogbeh yace ba haka abin yake ba. Ministan yace tun yanzu har Gwamnati ta kawo takin noma wanda ke da rahusa.

Gwamnatin tarayya na shirin kawo karshen karancin abinci da ake samu a cikin kasa Inji Mukaddashin shugaban Farfesa Yemi Osinbajo kwanaki. A dalilin haka ne aka ware makudan kudi Naira Miliyan 750 domin harkar gona a kasar.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...