Shugaba Buhari ya gana da Iyalin sa
A yanzu haka shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga
Fadar shugaban kasa da ke Aso Villa. Shugaban kasar ya iso filin jirgin sama na
Kaduna a Jirgin shugaban kasa, daga nan ya zarce zuwa Birnin Tarayya, dazu haka shugaban ya shiga Fadar Aso Villa.
Shugaba Muhammadu Buhari ya gana da iyalin sa;
Shugaban kasar ya hadu da Mai dakin sa Hajiya Aisha Buhari da kuma Uwargidar
Mataimakin shugaban kasa Misis Dolapo Osinbajo da wasu Jikokin sa.
Na samu sauki Inji Shugaba Buhari
Majiyar mu ta nuna mana cewa an yi wani dan karamin
biki domin shigowar shugaban kasar. Mun samu rahoton cewa shugaban kasar ya
gana da Ministocin sa a Fadar wanda daga ciki akwai Rotimi Amaechi.
Har wa yau dai mun ji labarin cewa shugaban kasar yace
jikin say a murmure, shugaban kasar yace yanzu yana jin kan sa wasai. Tun a
inda ya sauka wani Dan Jarida ya tambaye sa ko ya jikin sa, shugaba Buhari ya
fada masa cewa ai ga shi nan yana ganin sa.
No comments:
Post a Comment