Tuesday, March 21, 2017

Abin da ya sa El-Rufa’i ya rubutawa Buhari wasika



Ashe Shugaba Buhari ne ya nemi El-Rufa’i ya rubuto masa takarda




Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa’i ya rubuta wasika ga shugaba Muhammadu Buhari kwanaki inda ya fada masa cewa akwai gyara a tafiyar. Sai dai yanzu mun gano dalilin da ya Malam Nasir El-Rufa’i ya rubuta wannan takarda

Kwanan nan aka samu labarin cewa Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i ya rubuta wata wasika ga shugaban kasa Muhammadu Buhari inda yake kiran sa da yayi maza yayi wasu gyara a mulkin sa, ciki dai ana bukata ya sallami wasu na kusa da shi irin su Abba Kyari da Babachir Lawal.



El-rufa'i lokacin da ya kai ziyara Daura wajen Buhari


Sai dai bincike da wata Jarida tayi an gano cewa ashe shugaba Buhari ne da kan sa ya nemi Malam Nasir El-Rufa’i ya rubuta wannan takarda a sa’ilin da su ka hadu a Garin Daura lokacin bikin Sallah a Satumban bara.

Dama can an yi taro da Kungiyar Arewar nan ta ACF inda suka nemi a fadawa Buhari cewa ya tsige Sakataren Gwamnatin sa da kuma Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnati. Haka kuma Gwamna El-Rufa’i ya rubuta cikin takardar ta sa bayan nazari.

Rahotannin sun nuna cewa wasu na kusa da shugaban kasar ne su ka fito da takardar Duniya ta gani domin a dauka cewa Gwamna El-Rufa’i yana yi wa Shugaba Buhari zagon kasa ne. Wasu dai na ganin cewa siyasar tana kadawa ta wajen Gwamnan na Jihar Kaduna kuma suke kokari su taka masa birki.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...