Kusan mutane miliyan 3 na
Najeriya suka tafka muguwar asara bayan tsarin nan na MMM ya rushe Inji
shugaban Hukumar NDIC
Shugaban Hukumar NDIC Umaru Ibrahim yake bayyana cewa
‘Yan Najeriya kimanin miliyan 3 ne ta sha da su misilla bayan tsarin cacar nan
na MMM ya rushe. Umar Ibrahim yace ya samu wannan bayanan ne a kafafen yada
bayanai na zamani.
Idan ta tabbata kamar yadda ya zo a Jaridar Daily
Trust, Najeriya tayi asarar Naira biliyan 18 a tsarin nan na MMM mai nunka
kudi. Shugaban NDIC din ya bayyana haka ne a jiya wajen wani taro da aka yi a
kasuwar baja-kolin Duniya a Kaduna.
Tun dama can an gargadi ‘Yan Najeriya game da irin
wadannan tsare-tsare, sai dai Jama’a da dama suka yi kunnen-kashi, to ga irin
ta nan dai, yanzu makudan kudin Jama’a da dama ya tafi har abada.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment