Yayin da ake shirin bikin
cika shekara 80 a Duniya na tsohon shugaban kasar nan Olusegun Obasanjo, ya
kuma fito ya ba Jama’a mamaki inda yace kai bai ma san ko shekarun sa nawa ba.
Jiya ne tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya
bayyana cewa bai san ko asalin shekarun sa nawa ba. Obasanjo yace shi dai abin
da mahaifiyar sa ta fada masa shi ne an haife sa a ranar cin kasuwa.
Obasanjo yace bai san takamammen ranar da aka haife sa
ba domin iyayen sa ba su iya rubutu da karatu ba. Obasanjo yace mahaifiyar sa
ta shirya tafiya kasuwa ne kurum sai nakuda ya kama ta, a haka ne dai aka haifi
tsohon shugaban kasar.
Obasanjo ya bayyana haka ne yayin da yake ganawa da
yara inda ya rika raba masu kyautar littatafai a Garin sa da ke Abeokuta.
Obasanjo yace kawai dai ya kiyasta ranar haihuwar ne ko da yake ba na asali
bane, amma kusan lokacin da aka haife sa kenan.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment