Monday, March 20, 2017

Allah yayi: Man Utd ta motsa bayan wata shida



Man Utd ta tashi daga na 6 bayan rabin shekara




Kungiyar Man Utd ta tashi daga mataki na 6 wanda ta dade a kai a wannan makon. Yanzu haka Man Utd ta dawo mataki na 5 inda ta kerewa Kungiyar Arsenal. Sai dai abubuwa na iya cabewa idan Man City da sauran manya suka ci wasannin su.

Man Utd dai tayi nasara ne bayan ta doke Kungiyar M/Boro da ci 3-1. Wannan ne kusan wasa na farko bayan Kungiyar M/Boro ta kori Kocin ta wanda tsohon Mataimakin Koci Jose Mourinho na Man Utd ne Aitor Karanka.

Marouane Fellaini da Dan wasa Smalling su ka jefa kwallaye a raga. Shi ma dai Dan wasa Jese Lingard ya zura kwallo mai kyau. Alvaro Negredo na Kungiyar Boro ne ya ci wa Kungiyar kwallo guda. Man Utd dai ta kai kusan watanni 6 a mataki na 6 a gasar firimiya.



Kocin Man Utd Jose Mourinho



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...