Wednesday, March 1, 2017

Kocin Arsenal Wenger zai tashi?




Da alamu kwanakin Kocin kungiyar Arsenal Arsene Wenger sun zo karshe. Wata majiya tace har an fara kishin-kishin din wanda zai maye gurbin na sa.

Dama can Kocin Kungiyar Arsenal watau Arsene Wenger na fuskantar barazana da kalubale tun bayan da Kungiyar sa ta kwashi kashin ta a hannun Bayern Munich makonnin baya. Bayern Munich din dai ta koyawa Arsenal darasi da ci 5-1 a Gasar Champions League.

Kocin Juventus Massimiliano Allegri ya fadawa abokan sa a kasar Italiya cewa zai wuce Arsenal a karshen kakar bana domin ya karbi Koci Arsene Wenger. Da alamu kuma dai hakan za ayi watau Allegri zai bar Juventus din da yake horaswa.

Allegri dai ya dade yana horaswa a Italiya har ya kuwa ci kofin gasar Seria A tare da AC Milan da kuma Kungiyar Juventus. Koci Arsene Wenger dai yace ko zai bar Arsenal ba zai bar aikin horaswa ba sai nan gaba.

Wasu suna ganin ya kamata Kocin ya tattara kayan sa ya bar Kulob din don kuwa duk shekara Arsenal din ba ta kai ko ina. Shekaru fiye da 20 kenan Wenger ya kwashe a Arsenal.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...