Da
alamu kwanakin Kocin kungiyar Arsenal Arsene Wenger sun zo karshe. Wata majiya
tace har an fara kishin-kishin din wanda zai maye gurbin na sa.
Dama
can Kocin Kungiyar Arsenal watau Arsene Wenger na fuskantar barazana da
kalubale tun bayan da Kungiyar sa ta kwashi kashin ta a hannun Bayern Munich
makonnin baya. Bayern Munich din dai ta koyawa Arsenal darasi da ci 5-1 a Gasar
Champions League.
Kocin
Juventus Massimiliano Allegri ya fadawa abokan sa a kasar Italiya cewa zai wuce
Arsenal a karshen kakar bana domin ya karbi Koci Arsene Wenger. Da alamu kuma
dai hakan za ayi watau Allegri zai bar Juventus din da yake horaswa.
Allegri
dai ya dade yana horaswa a Italiya har ya kuwa ci kofin gasar Seria A tare da AC Milan da kuma
Kungiyar Juventus. Koci Arsene Wenger dai yace ko zai bar Arsenal ba zai bar
aikin horaswa ba sai nan gaba.
Wasu
suna ganin ya kamata Kocin ya tattara kayan sa ya bar Kulob din don kuwa duk
shekara Arsenal din ba ta kai ko ina. Shekaru fiye da 20 kenan Wenger ya kwashe
a Arsenal.
No comments:
Post a Comment