Hukumar
JAMB mai gudanar da jarrabawar shiga makarantu na gaba da Sakandare na ta kawo
sabon tsari. Yanzu haka dai an rage wa’adin yin rajistar jarrabawar JAMB din.
Hukumar JAMB ta rage lokacin da ake dauka wajen yin rajista domin
rubuta jarrabawar ta shiga Makarantun gaba da Sakandare a kasar. JAMB tace daga
yanzu wata guda kurum za a bada domin yin rajista.
Shugaban Hukumar JAMB din
Farfesa Ishaq Oloyede yace za a fara sayar da takardun jarrabawar ne a Ranar 20
ga wannan Watan, sannan kuma za a rufe saidawa a Ranar 19 ga Watan Afrilun
gobe. Yanzu haka dai ana so har Makafi su fara zana jarrabawar.
Farfesa Oloyede ya bayyana
haka ne a Legas yace wannan karo ba za a dauki dogon lokacin nan har na watanni
uku ana rajista ba. Farfesan yace kuma ba za a kara wa’adin ba nan gaba don
haka sai kowa ya garzaya yayi abin da ake bukata cikin lokaci.
Yanzu dai ana yin jarrabawar
JAMB din ne da na’ura mai kwakwalwa. Za kuma a yi wani gwaji ga duk mai bukata
domin shiryawa Jarrabawar da kyau Inji Hukumar, ko da yake dai ba tilas bane
yin gwajin.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment