Wednesday, March 1, 2017

An yi kira ga Musulmai su rike Al-Kur’ani


Wasu Malamai daga kasar Saudiyya sun yi kira ga Musulmai suyi riko da littafin Al-Kur’ani mai girma domin su rabota a nan Duniya da lahira.



Wasu Malaman addini da suka taso tun daga kasar Saudiyya sun yi kira ga Jama’a suyi riko da Littafin Al-Kur’ani mai girma. Malaman suka ce riko da littafin Allah ne kadai zai kai Jama’a ga shiriya Duniya da kuma Lahira.

Malaman dai sun taso ne daga Jami’ar Ummul-Qura ta cikin Birnin Makkah da ke Kasar Saudiyya inda suka zo Najeriya kuma Jihar Kaduna. Sun zabi wurare inda suka yi wa’azi a Jihar daga ciki akwai masallacin ITN da ke Zangon-Shanu Zaria.



Dr. Ahmad Al-Furaih da kuma Dr. Ahmad Al-Huraisi da ke Jami’ar Birnin Makkah suka ce dole a komawa Littafin mai tsarki  domin a samu cigaba a nan da ma gaba. Daya daga cikin Malaman yace idan har makarantun Kur’ani suka lalace to al’umma ta lalace koda yake dai mutanen Najeriya suna da kokarin karatun Al-kur’ani.

Dr. Al-Huraisi yayi kira da Jama’a su yi koyi da darussan da ke cikin Al-Kur’ani irin na kisosshin Annabawa. Riko da littafin dai bai tsaya a karatu ba kurum, ya hada har da aiki da shi Inji Malaman kamar yadda mutanen da su gabace mu suka yi.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...