Friday, March 31, 2017

Tattalin arziki: IMF ta jinjinawa Najeriya

IMF ta Duniya ta jinjinawa Gwamnatin Najeriya




IMF ta Duniya ta jinjinawa Najeriya wajen kokarin da tayi wajen fara shawo kan tattalin arzikin kasar wanda ya ruguje a shekaran bara

IMF mai bada lamuni ga kasashen Duniya ta yabawa Najeriya wajen irin kokarin da tayi na shawo kan matsalar tattalin arziki musamman wajen daidaita darajar kudin kasar na Naira wanda ya rugurguje.

Bankin kasar na CBN ya saki sama da Dala Biliyan guda ga bankuna domin farashin dalar yayi sauki a kasar. Wannan tsari da CBN ta kawo dai yayi aiki bayan a da ana tunani cewa Dalar na iya zarce N1000.

IMF din ta jinjinawa tsarin tattalin arzikin kasar inda ta ke fatan nan gaba ma abubuwa su kara kyau. IMF dai na neman ganin yadda za ayi masu jari su shigo kasar su ba-ja-kolin su. IMF din mai bada lamuni tace Najeriya na kan hanyar da ta dace.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...