IMF ta Duniya ta jinjinawa Gwamnatin Najeriya
IMF ta Duniya ta jinjinawa
Najeriya wajen kokarin da tayi wajen fara shawo kan tattalin arzikin kasar
wanda ya ruguje a shekaran bara
IMF mai bada lamuni ga kasashen Duniya ta yabawa
Najeriya wajen irin kokarin da tayi na shawo kan matsalar tattalin arziki
musamman wajen daidaita darajar kudin kasar na Naira wanda ya rugurguje.
Bankin kasar na CBN ya saki sama da Dala Biliyan guda
ga bankuna domin farashin dalar yayi sauki a kasar. Wannan tsari da CBN ta kawo
dai yayi aiki bayan a da ana tunani cewa Dalar na iya zarce N1000.
IMF din ta jinjinawa tsarin tattalin arzikin kasar
inda ta ke fatan nan gaba ma abubuwa su kara kyau. IMF dai na neman ganin yadda
za ayi masu jari su shigo kasar su ba-ja-kolin su. IMF din mai bada lamuni tace
Najeriya na kan hanyar da ta dace.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment