Monday, March 13, 2017

Shugaba Buhari zai yi zazzaga




Buhari zai yi kakkaba a Gwamnati; Za a canza wasu Ministoci Inji Sahara Reporters


 -- Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yi babban sauyi a Gwamnatin sa -- Za a canza wasu Ministoci da manyan Jami’an Gwamnati -- Zazzagar za ta taba wasu manyan kusoshi






Kusan shekaru biyu kenan da kafuwar wannan Gwamnati ta shugaba Muhammadu Buhari, mun samu labari cewa za a yi wasu sauye-sauye a Gwamnatin kwanan nan ba da dadewa ba. Sai dai Majiyar ba ta bayyana sunayen wadanda abin zai taba ba. Za dai a ga shakuwar aiki kwarai tsakanin shugaban kasar da Mataimakin sa bayan nan.

Majiyar da tayi magana a boye saboda yanayin kakkabar, tace cikin wadanda za a taba akwai manyan kusoshin da ke kusa da shugaban kasa Muhammadu Buhari. Sannan kuma dai Gwamnan CBN Godwin Emifiele yana cikin wadanda za su iya bada wuri.


Za kuma dai a cike guraben Ministocin Jihar Kogi da Gombe, wanda daya ya mutu yayin da daya kuma ta bar aikin zuwa Majalisar dinkin Duniya. Za kuma dai a sauya guraben Ministocin da ba su jituwa.

Ba mamaki kuma a rage wa Ministan ayyuka da wuta da gidaje Babatunde Fashola aiki a sauyin da za a gani. Cikin kusoshin da za su iya tafiya dai akwai Abba Kyari da kuma Babachir Lawal watau shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnati da Sakataren Gwamnati. Sai dai mai magana da bakin shugaban kasar yace bai san maganar ba.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...