An dai ga abin ban mamaki a
Majalisar Dattawa wannan mako yayin da wani Dattijo yayi kememe ya ki bin umarnin
Sanatocin. Dattijon yace: 'Ba za a rera National
anthem din ba...'
Kwanan nan ne fadar shugaban kasa ta tura sunan wani
zuwa ga Majalisa a matsayin Jakadan Najeriya. Ko da wannan Dattijo ya shiga
Majalisar an ga abin mamaki a yayin tantance sa.
Sylvanus Nsofor mai shekaru 82 a Duniya tsohon Alkali
ne a babban kotun kasar da kuma kotun daukaka kara duk na Najeriya, Nsofor ya
kuma koyar a wata Kwalejin shari’a da ke Birnin Landan watau a kasar Ingila.
An dai aika sunan sa a matsayin daya daga cikin
Jakadun kasar zuwa ga Sanatoci domin su tantance sa. Ko da Dattijon ya hallara
gaban masu tantancewar sai wani Sanatan Jihar Legas Gbenga Ashfa ya nemi tsohon
ya karanta taken kasar. Nan fa wannan tsoho mai sama da shekaru 80 a Duniya
yace ba zai rera taken ba, hakan kuma aka kyale sa.
An dai haifi tsohon Alkali Sylvanus Nsofor a Garin
Oguta na Jihar Imo a watan Maris na shekarar 1935 watau shekaru sama da 20
kafin Najeriya ta samu ‘Yancin-kai. Za a tura Mista Nsofor aikin jakadanci zuwa
wata kasa.
No comments:
Post a Comment