Saturday, March 4, 2017

HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN



HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN-ZARIA





Ni’imar Musulunci-Daga Bakin Imam Sheikh S. S Abubakar


A’udhu BilLahi minasshaidan Ar-Rajim, BismilLahir Rahman Ar-Raheem,
Dukkan Godiya sun tabbata ga Allah SWT Mai iko da daukaka, Gwamnin Sarki mai hikima mai adalci sannan Masani a cikin al’amuran Sa. Muna shaidawa lallai babu abin bauta da gaskiya face Allah SWT; Wannan shaidawa ce wanda muke fata a dalilin ta mu samu tsira daga azaba mai radadi. Kuma muna shaidawa lallai Shugaban mu, Annabi Muhammad SAW, Bawan Allah ne kuma Manzon ne Wanda aka aiko da gaskiya.

Bayan haka:
Hakika Allah yayi mana ni’ima da wasu ni’imomi masu dinbin yawa; idan da za mu lissafa su duk, to ba za mu iya ba. Daga ciki akwai ni’imar ji, gani, hankali, lafiya, dukiya, ‘ya ‘ya, iyali; mace da namiji, da kuma wasu masu dinbim yawa dabam. Sai dai duka wadannan ni’imomi suna karewa ne yayin da rayuwa ta kare. Amma akwai ni’ima guda wanda ke dogewa har ga lahira; ita ce mafi girmar ni’ima watau ni’imar musulunci. Don ita wannan ni’ima ita ke bambanta tsakanin mai imani da rafkananne, tsakanin mai biyayya da mai sabo, tsakanin Musulmi da kuma kafiri. Saboda haka tasirin wannan ni’ima na bayyana a nan Duniya da kuma lokacin mutuwa da kuma Lahira. Shi musulunci shine Addinin da Allah ya zaba mana ya kuma yardawa bayin sa a lokacin da Annabi SAW yake aikin hajjin sa na ban-kwana.  Allah SWT yace: A yau na kammala maku addinin ku, na kuma cika maku ni’ima ta, na kuma yardarm maku musulunci a matsayin addinin ku. Malamai suka ce ‘Ni’ima Ta’ a wannan ayar ita ce musulunci.

Madalla da wannan baiwa da wannan ni’ima ta Allah da ya kammala mana addini. A Duniya abin da ake nufi da musulunta shi ne a ce mutum na bin tafarkin shari’ar Allah a rayuwa. Allah SWT ya halicce mu ya kuma saka mu kalifofin sa a bayan kasa domin kawai mu aiwatar da tafarkin sa a doron kasa. Ko a Duniya sai ka ji ance an aika wani a matsayin jakadan Najeriya a wuri kaza, duk wanda aka aika jakada, abin da ake so a gare sa shi ne ya kare muradu ya kuma tafiyar da manufar Najeriya a wannan kasar da aka aika sa. Saboda haka abin da Allah SWT yake so a gare mu shi ne mu tafiyar da rayuwar mu ga shari’ar sa a cikin kowane al’amari daga cikin al’amurran rayuwar mu. Abin da ake so komai za muyi ya zama mun samu lada saboda mun yi tamkar yadda Allah yace; duk abin da aka yi kamar yadda Allah yace aka kuma yi domin kuma yardar sa to ya zama ibada. Allah madaukaki yake cewa: ‘Ban hallici aljannu da mutane ba face don su bauta mani…’ Watau yadda Allah yace kuma domin neman yardar sa. Madalla dai da wannan ni’ima da Allah ya zabe mu a matsayin al’umma ta tauhidi wadanda za su daukaka kalmar ‘La-ila-ha-illal-Lah. A kan wannan ne dai aka riko aiko da Annabawa. Da ace za mu rika godiya ga Allah muna masu sujuda har zuwa tashin kiyama, ba za mu iya abin da ya dace na godiya ba.

Allah madaukakin Sarki ya fada a cikin Al-kur’ani ga Manzon Sa cewa: ‘Wasu har suna goranta maka (watau Annabi SAW) cewa sun musulunta tamkar sun yi maka wata alfarma….’ Ka (Kai Annabi SAW) fada masu cewa: ‘ka da ku goranta mani musuluncin ku, ni ku ka yi wa alfarma ko ni nayi maku alfarma?’ Bari Allah ne ya shiryar da ku zuwa ga imani. Wannan shi ne gaskiyar lamari idan har kun tabbata masu imani’ Saboda haka dai ni’imonin Allah SWT suna da yawa amma wannan ni’ima wanda Allah yayi mana baiwa da ita, ita ce babbar ni’ima. Allah SWT fa ya riga ya fada cewa: Addini karbabbe a wajen Allah shine Musulunci; don haka Allah ba zai karba daga wani ba addini dabam idan ba musulunci ba, kana a Lahira zai zama cikin masu asara. Allah yayi mana ni’ima wanda a dalilin ta ya fada mana cewa Ku (Musulmai) kun kasance mafificiyar al’umma da Ubangiji ya fitar a doron kasa domin amfanin mutane… kuma dai kullum za ku rika umarni ga alheri tare da hani daga mummuna… Wannan dai shi ne ya mayar da ku dabam cikin sauran al’umma.

Sai dai kuma fa imani ba ya kasancewa ta hanyar buri ko magana da baki ko takama da ado da sunan musulunci kadai. Malamai suka ce imani shi ne abin da ya tabbata a cikin zuciya kana kuma aikin mutum ya gaskata haka. Idan ya zamana kana takamar kai musulmi ne amma ka buge da ayyukan assha, to ina musuluncin? Ka ga watau dole muyi bakin ciki a wannan lokaci saboda irin yadda mutane Musulmai su ke aikata aiki na assha, cin amana da barna a wurare da dama. Wannan abin takaici ne wanda ya shafi mutane tun daga saman su har kasa; watau ba wadanda ke rike da manyan mukamai kurum suke da wannan hali ba, har wani da kake ganin sa abin tausayi yana da irin wannan hali, yana kokari ya ci amanar wani har ma ya iya kashe wani. Duk a haka dai muna cewa mu musulmai ne. Wane irin musulunci ne wannan? Idan har mun yarda cewa mu musulmai ne wadanda Allah yayi mana ni’ima, to mu rike musuluncin nan mana; a gidajen mu da sauran wuraren mu, ya zama duk wanda muka yi mu’amala da shi zai ce mun fita dabam, mu kuma muna fada masa cewa ai musulunci ne wannan! Don me ba zai kasance haka ba? Don me za a wayi gari har Musulmi yace gara ya ba Kafiri amana don musulmi bai da rike-amana. Wannan musiba ce! Me zai hana mu tambaya idan har ba mu san wannan addini ba, har ya zama shi muke yi tare da iyalan mu da makwabtan mu da sauran wuraren ayyukan mu?

Saboda haka ‘Dan uwa musulmi mu godewa Allah da wannan ni’ima, mu sani fa ba kurum cewa nagode bane. A’a dole mu yabi Allah muyi godiya sannan a ga muna da’a wanda shi ne babban godiya. Hakika shi Manzon Allah SAW an umarce sa da cewa: ‘Lallai salla ta da duk yanka ta da rayuwa ta da mutuwa ta… Zan yi su ne ga Allah Ubangiji babu wani abokin tarayya a gare Sa… da haka aka yi mani umarni kuma Ni ne farkon wanda ya mika wayau watau Musulmi’. Haka aka umarci Manzo SAW wannan ya sa duk mai hankali ya kamata yayi koyi da wannan. Ana so duk abin da musulmi yake aikatawa idan ka tambaye sa, ya fada maka cewa wannan shari’ar musulunci ce; haka ake zama musulmi!




Allah ka ba mu fahimtar Addinin musulunci sannan ka tseratar da ni da ku duka daga azaba mai radadi ka shigar da mu gida na ni’ima. Allah ya karbi ayyukan mu tare da dadin tsira ga Annabin Mu da Iyalan Sa da wadanda suka yi imani da Shi zuwa Ranar karshe. Allah ka tabbatar da yardar ka kalifofin Manzon Allah SAW hudu da sauran sahabai, Ka samu cikin Mabiyan Su. Allah ka buwayar da addinin musulunci ka rusa abokan gaban sa. Allah ka ba mu zama lafiya ka raya mana kasa cikin alheri ka tsrerar da mu daga duk wata fitina. Allah ka jagoranci shugabannin mu zuwa abin da kake so ka kuma yarda da shi. Allah ka ba mu ka kara mana lafiya ka jikan wadanda suka rasu. Allah ka ba shugaban kasar mu lafiya ka dawo mana da shi lafiya.




Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Muhammadmalumfashi@gmail.com          
Twitter: @Ya_waliyyi


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...