– Najeriya
na fama da durkushewar tattalin arziki
–
Sai dai an kusa fita daga cikin wannan radadi Inji
fadar shugaban kasa
– Alkaluma
sun nuna cewa Najeriya na farfadowa
Fadar shugaban kasa
tace Najeriya ta kama hanyar fita daga radadin tattalin arzikin da ake ciki.
Najeriya dai na fama da durkushewar tattalin arziki tun bara bayan farashin mai
ya rushe.
Alkaluman bincike su
nuna cewa Najeriya na yin gaba idan aka yi la’akari da jimilar kudin kasar na
GDP na karshen wancan shekarar. Mai ba shugaban kasa shawara game da harkokin
tattalin arziki Dr. Adeyemi Dipeolu ya bayyana haka Inji mai magana da bakin
mukaddashin shugaban kasa.
Najeriya dai ta samu
ci-bayan tattalin arziki ko da dai bai kai yadda aka sa rai na tabarbarewar ba.
Dr. Dipeolu yace alkaluman sun nuna cewa kasar na kokarin fita daga cikin halin
durkushewar arzikin da ta ke ciki.
Kamfanin man Najeriya
na NNPC ya bayyana cewa man da kasar nan ke hakowa a kowace rana ya kara yawa.
Ana samun gangar mai
sama da miliyan 2. Da alamu dai rikicin yankin na Neja-Delta yayi kasa. Shugaban Kungiyar OPEC Sanusi
Barkindo yace yayi mamakin yadda Najeriya ta tsira daga kangin da aka shiga na
tattalin arziki bayan da mai yayi kasa.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment