HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN-ZARIA
Godiya ga ni’imar Allah daga Bakin Imam Sheikh S. S Abubakar
A’udhu BilLahi minasshaidan
Ar-Rajim, BismilLahir Rahman Ar-Raheem,
Dukkan Godiya sun tabbata ga
Allah SWT, shi ne mai karamci da baiwa ga bayin Sa. Muna godiya da yabo gare sa Madaukakin
Sarki.
Shi ne mai yin falala dabam-dabam ga bayin sa da kuma nau’o’i dabam-dabam na
ni’ima. Muna shaidawa lallai babu abin bauta da gaskiya face Allah SWT, Shi
kadai yake, babu abokin tarayya a gare Sa. Muna shaidawa lallai
Shugaban mu, Annabi Muhammad SAW Bawan Allah ne kuma Manzon Sa ne.
Bayan haka:
Ya ku ‘Yan uwa mu ji tsoron Allah Madaukakin Sarki kuma mu gode maSa
bisa ni’imomin da yayi mana, mu kuma sani cewa Allah ne kadai mai ni’ima kuma
gare Sa muke fatar ayi mana ni’ima a Duniya da kuma lahira. Allah SWT yana cewa:
Idan ku kace za ku kidaya ni’imomi na, ba
za ku iya lissafe su ba. Lallai Allah mai yawan gafara ne mai kuma yawan
jin-kai.
Saboda haka Bayin Allah ku gode masa bisa ni’imomin da
yayi maku domin kuwa godiya na daga cikin dalilan su ke sa Allah ya kara kuma
ya wanzar da ni’ima. Don saboda kafircewa ni’imar Allah kuma sai ya zama
ni’imar nan ta tawaya ko kuma ta gushe gaba daya. Allah SWT yana cewa a
Kur’ani: Idan ku ka gode, lallai Ni zan
kara maku...Lallai kuma idan har ku ka kafirce, azaba ta tana da tsanani. Allah
Mai tsarki yana dada fada a cikin Kur’ani inda ya bada misali da wata Al-karya Yake
cewa tana cikin aminci da kwanciyar hankali da arziki, amma sai su ka kafirce
daga ni’imomin Allah, sai kuwa aka dandana masu tufafin yunwa da tsoro saboda
abin da suka kasance suna aikatawa na kafirci.
Ya ku ‘yan uwa ya ake godewa Allah da ni’imomin sa?
Wannan yana cikin dagewa wajen bin umarnin Ubangiji Ta’ala muddin aka ce Allah
yayi umarni a aikata kaza ko a bari sai mutum yayi iyawar sa ya aikata ko ya
bari in dai har wannan umarni ya zo daga Littafin Allah ko bakin Annabin Sa
SAW. Lallai fa mai sabon Allah ba mai godiya bane ga Ubangiji ko da ya ta furta
cewa ‘Na godewa Allah.’ Ina amfanin mutumin da ke fada da harshe cewa yana
godiya alhali yana ta sabawa Allah? Ko shin wannan mutumi ba ya tsoro a ce da
shi karya ka ke yi. Allah SWT da ya tashi sai ya hallice ka mutum kuma mai hankali,
sannan kuma ya ba ka musulunci da sauran ni’imomi, don haka Ubangiji ya
cancanci godiya. Mu sani dai cewa mafi girman ni’ima kenan shiriya zuwa ga
Musulunci. A yayin da ku ke Musulmai masu imani wasu na can suna dimuwa; wasu
na cikin fushin Ubangiji na take sani, wasu kuma na cikin duhun Jahilci ba su
ma gane wanene Ubangiji ba. Saboda haka duk wanda Allah ya azurta da Musulunci
ya samu abu biyu; sanin gaskiya da kuma biyayya gare ta. Wannan ya bambanta
mutum da Yahudu da su ka take sani da kuma Nasara da ba su san gaskiya ba su ke
cikin duhun jahilci.
Manzon Allah SAW ya nuna mana yadda ake godiya ga Allah
SWT ban da irin Salloli da yake yi, duk wani karamin abu sai Manzo SAW ya
godewa Allah. Sai mu tambayi kan mu kamar yadda Annabi SAW yake tsayawa Sallar
Nafila cikin dare, shin kai raka’a nawa kayi jiya cikin dare domin nuna godiyar
ka ga Allah? Manzon Allah ya kan yi addu’ar godiya ga Allah da ya raya sa kuma
bayan ya tashi daga barci. Kai ko jiya da ka farka ka fadi haka? Ko ba ka san
cewa ni’ima ba ce da Ubangiji Ta’ala ya farkar da kai bayan ka kwanta. Ko da ka
shiga ban-daki ka yi uzuri ka fito cikin sauki kayi irin abin da Annabi SAW
yake yi? Annabi SAW yana addu’ar godiya ga Allah da ya samu damar kawar da abin
da ke cikin jikin sa. Sannan Manzon Allah SAW ya kasance idan ya ci abinci (duk
da Annabi SAW ba ya cin wani abinci sosai) yana godiya ga Allah iri
dabam-dabam. Kai yau bayan ka karya kumallo da safe mai ka fada na godiya, watakila
har da gyatsa kayi. Ko ba ka dauka cewa kokon da kosai da ka samu ni’ima bane?
Wani bai samu ko kokon da ka samu ba domin ya sha, wani kuma ga kokon amma bai
isa ya sha ba saboda wani hali na rahin lafiya ko aminci. Haka kuma Manzon
Allah SAW yake yi idan zai kwanta barci cikin yini, watau dai kullum Manzon Allah
cikin godiya yake. Shin mu haka muke? Ya kamata muyi koyi da Manzon mu Annabi
SAW. Mu sani cewa duk wata ni’ima daga gare sa ta ke; babu mai badawa ko hanawa
face shi. Idan har ka rasa wata ni’ima ta Duniya ka da ka zargi kowa kana cewa
‘Wane ya hani ni’, Allah Madaukaki ne bai ga dama ba. Haka kuma idan Allah
Madaukaki ya ba ka kar ka butulce masa kana ‘Wane ya bani’, ba kowa bane shi
face dan-aike. Allah SAW yana cewa a Kurani cewa: Duk abin da ku ka gani na ni’ima daga Allah ne, don kar ka dauka
wani ya isa ko dabarar mu ce!
Allah ka ba mu fahimtar
Addini ya
sa ya
amfane
mu gaba daya. Allah ya karba mana ya tseratar da mu daga azabar wuta mai radadi, ya shigar da mu
cikin gidan ni’ima. Allah yayi dadin tsira ga Annabin mu Muhammad SAW da Iyalan
Sa da Sahaban Sa musamman Khalifofin Sa shiryayyu.
Allah ka taimaki Musulunci da Musulmai ka kuma kaskantar
da Kafirci da Kafirai. Allah ka kare mu daga wata fitina da damuwa. Allah ka
kara mana ni’imar ka da samun yardar ka. Allah ka tara mu a kiyama tare da Annabawan
ka da kuma zababbun bayin ka.
Allah ka taimaki kasar mu ka
taimaki shugabannin mu; ka kama hannayen su ka wanzar da al’amurar su. Allah ka shiryar mana da su ga
abin da kake so kuma ka yarda da shi.
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga
Masallacin I.T.N-Zaria.
Twitter: @Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment