Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya
kira Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello a wayar tarho daga Landan. Ga dai yadda ta
wakana tsakanin shugaban kasar da Gwamna Bello.
Mun
samu labari cewa shugaba Buhari wanda ke Birnin Landan inda yake hutawa yayi
waya da Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello. Majiyar tace shugaba Buhari ya matsu
ya dawo Najeriya domin ya cigaba da aiki.
Shugaban
kasar ya kira Gwamnan Jihar Kogi ne lokacin yana tare da kakakin Majalisa da
kuma wasu Kwamishinonin sa. Shugaba Buhari ya gode da kokarin Jama’a da ke tayi
masa addu’a a ko yaushe.
Haka
kuma Muhammadu Buhari ya kira tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo a
wayar tarho daga Landan domin taya sa murnar zagayowar ranar haihuwar sa.
Obasanjo ya cika shekaru 80 da haihuwa a jiya.
Idan muka koma wani
bangaren kuma, dubban mutane ne suka fito suka yi wa shugaban kasar Najeriya
Muhammadu Buhari addu’a ubangiji ya maido sa lafiya a Birnin Zazzau. Yanzu haka
dai shugaba Buhari ya share fiye da wata guda da rabi a Landan.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment