Wasu sun raunata yayin da aka samu
wani arangama tsakanin Sojoji da ‘Yan Shi’a a Garin Katsina.
Mutane
3 sun samu rauni yayin da wasu Sojoji suka dura gidan wani shugaban shi’a a
Jihar Katsina. A yau din ne dai Sojoji suka dura gidan wani shugaban mabiya addinin
Shi’a Sheikh Yakubu Yahaya.
Shugaban
mabiyan na Shi’a Sheikh Yakubu Yahaya ya bayyanawa Jaridar Daily Trust cewa ba
shakka Jami’an tsaro sun kai masu hari har suka raunata wasu dama. Ciki dai
akwai wanda ya karya hakora, wasu kuma suka samu raunuka dabam-dabam a hannuwa.
‘Yan
Shi’an dai sun ce Jami’an tsaron sun zo ne da niyyar kisan gilla kamar dai yadda
aka addabe su tun kwana biyu da suka wuce. Mai magana da bakin ‘Yan Shi’an yace
Sojojin sun kai masu irin wannan hari a Garin Jos kwanaki. Jami’in ‘Yan Sanda
na yankin ya dai ce za ayi bincike game da lamarin amma har yanzu shiru.
Farkon
makon nan Femi Falana SAN Lauyan shugaban kungiyar IMN Ibrahim Az-Zakzaky, ya
rubuta wasika ga Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo SAN da kuma Ministan
shari’a na kasar Abubakar Malami SAN game da cigaba da daure malamin. Falana
yace idan har gwamnati ba ta saki Zakzaky ba zai dauki mataki.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment