Wednesday, March 1, 2017

Ko ka san ganga nawa ake hakowa a kullum?



– Yawan man da Najeriya ke samu ya kara yawa


Da alamu an rage samun fasa bututun mai daga yankin Neja-Delta


– A cikin ‘yan kwanakin nan dai har Naira ta tashi




Kamfanin man Najeriya na NNPC ya bayyana cewa man da kasar nan ke hakowa a kowace rana ya kara yawa. NNPC tace a kullum Najeriya na samun gangar mai sama da miliyan 2. Ko da yake dai ba bayyana dalilin karin ba.

Shugaban Kamfanin na NNPC Maikanti Baru ya bayyana haka yayin da ya zanta da ‘Yan jarida a Abuja. Mista Baru yace ana sa ran zuwa karshen shekara a rika samun sama da ganga miliyan 2.2 a kowace rana.

Da alamu dai rikicin yankin na Neja-Delta yayi kasa don kuwa kwana biyu ba a fasa wani bututun mai ba. Mukaddashin shugaban kasa Farfesa Osinbajo dai yayi ta ziyarar yankin kwanki domin kawo karshen rikicin.

Shugaban OPEC M. Sanusi Barkindo yace yayi mamakin yadda Najeriya ta tsira daga kangin da aka shiga na tattalin arziki bayan da mai yayi kasa. Barkindo yace yanzu haka an yi mai wuyar don kuwa farashin mai ya daga a duniya.

[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...