Mukaddashin shugaban kasa
Farfesa Yemi Osinbajo ya cika shekaru 60 a Duniya da haihuwa a yau Laraba 8 ga
watan Maris. Muna taya shugaban kasa na rikon kwarya murnar zagayowar ranar
haihuwar sa.
A yau ne Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo yake
cika shekaru 60 a Duniya. Osinbajo dai ke rike da Najeriya tun bayan tafiyar
shugaba Buhari a tsakiyar watan Junairu. Jama’a na ta kara yabawa Farfesan inda
suka ce bai ba da kunya ba.
Osinbajo ya tashi tsaye wajen harkar gyara tattalin
arzikin kasar da kuma sawwake harkar kasuwanci. A jiya ne ma dai aka kaddamar
da aikin jirgin kasan Legas da gwamnatin Buhari tayi alkawari. Mukaddashin ya
kuma kewaya Yankin Neja-Delta domin kawu karshen rikicin yankin.
Kwanan nan shugaban kasar na rikon-kwarya ya bayyana
yadda wannan gwamnati za tayi kokari wajen kawo karshen cin hanci da rashawa a
Najeriya. Osinbajo yace za a bi irin matakan da suka bi lokacin yana
Kwamishinan shari’a a Jihar Legas.
Kakakin Majalisa Rt. Hon. Yakubu Dogara ya taya
Osinbajo murnar wannan rana inda yace tabbas Osinbajo ya nunawa kasa da Duniya
cewa ya san me yake yi. Kwanaki aka nadawa Farfesa Yemi
Osinbajo Sarautar ‘Obong Emem’ na Garin Akwa Ibom.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment