Sunday, March 26, 2017

Ana kokarin ganin an hana bara a Arewa


Ana kokarin ganin an hana Almajiranci a Arewa



Muhammad Malumfashi ya halarci taron

Wata kungiya mai suna YouthHubAfrica na kokarin ganin yadda za a kawo karshen cin zarafin kananan yara da ake yi a kasar nan musamman a Arewacin Najeriya. Don haka ne ma dai aka shirya wani taro na karawa juna sani na kwanaki 3 a Garin Kaduna wanda NAIJ.com ta samu halarta.

‘Yan Jarida da sauran ma’aikata masu ruwa da tsaki daga Jihohin Kaduna, Kano, Sokoto, Kebbi har ma da Jihar Oyo su ka halarci taron. Ana dai kokarin ganin yadda Majalisun Jihohi za su kafa wannan dokar nan da ta kare hakkin kananan yarada kuma dabbaka ta.



Bukky Shonibare a wajen taron

Dokar za ta ba ‘ya ‘ya ‘yancin su auri wanda su ke so idan har sun girma sannan kuma a ba su ilmi mai inganci tare da haramta masu talla da yawan bara wanda hakan ke haifar da ‘da mara ido a al’umma.

An dai gayyaci manyan mutane inda suka gabatar da lacca da kasida game da batun. A mafi yawan Jihohin Arewa dai ba a kafa wannan doka da za ta ba yara ‘yancin su ba. Wanda ba shakka wannan na cikin abubuwan da ke maido mu baya kamar yadda Mawaki ya fada.



Taron karawa juna sani da YouthHubAfrica su ka gudanar a Kaduna


[NAIJ Hausa]

1 comment:

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...