– Sai
ga Shugaba Buhari a cikin ajin dalibai
– Shugaba
Buhari ya kai ziyara Jihar Edo inda ya kaddamar da ayyukan Gwamna Adams
Oshiomole
– Oba na Benin yace Shugaba Buhari na kokari wajen fada
da cin hanci a Kasar nan
Sai ga Shugaban Kasa
Muhammadu Buhari cikin aji tare da daliban Sakandare, shin ko ya je rubuta
takardar da ‘Yan adawa suka ce ba shi da ita ne na shaidar WASSCE watau ta
kammala Sakandare? Abin mamaki kuma an ga Shugaba Buhari yana rubutu cikin wani
littafi, ko dai jinga ne Malam ya bada?
A cikin ajin dai Shugaba
Buhari ya zauna tare da Gwamnan Jihar kan sa, Adams Oshiomole daga gefen sa.
Daliban dai sun kasance suna ta kurawa Shugaban Kasar Najeriya ido yayin da ya
zauna cikin su. Ko yana rubuta sunayen masu surutu ne a ajin, ko kuwa yana
bincika wadanda ba su halarci darasi ba ne?
Shugaba Buhari ya kai ziyarar
kwana biyu Jihar Edo inda ya kaddamar da ayyukan Gwamna Adams Oshiomole mai
shirin barin gado, ciki har da Makarantar New
Era Secondary School da aka maida
Samuel Ogbemudia Secondary School.
Shugaba Buhari ya kuma kai
ziyara wajen sabon Sarki, inda ya taya Sarkin murna, wanda shine Oba ne Benin
na 40 a Jerin sarautar. Shugaba Buhari
ya tunawa Jama’a cewa ya zauna a wannan gari na Benin na wata da watanni bayan an masa juyin mulki. Oba na Benin
din ya godewa Shugaba Buhari.
Gwamna Oshiomole na kokarin satar amsar Baba Buhari :P
Hahaha aiko dai gashinan yana yin dagon wuya.
ReplyDelete