Gwamna Oshiomole ya sauka daga Gwamnan Jihar Edo
– A jiya aka nada Mista Godwin Obaseki a matsayin sabon Gwamna na Jihar Edo
– Wa’adin Tsohon Gwamna Adams Oshiomole ya kare
– Sabon Gwamna Obaseki ya yabawa mai barin-gado Adams Oshiomole yace anyi namiji
A jiya Asabar aka nada Sabon
Gwamna a Jihar Edo. Mista Godwin N. Obaseki ya zama Sabon Gwamna na Jihar bayan
wa’adin Tsohon Gwamna Adams Oshiomole ya kare. Gwamna Obaseki ya yabawa
Kwamared Adams Oshiomole da irin ayyukan da ya zuba a Jihar.
Obaseki yace Gwamna
mai-barin-gado Adams Oshiomole yayi namijin kokari wajen ganin ya canza Jihar
Edo. Babban Alkalin Jihar, Alkali Cronwell Idanosa ya rantsar da Gwamnan,
Godwin Obaseki da kuma Mataimakin Sa, Phillip Shu’aibu.
Mutane da dama sun halarci
taron rantsar da sabon Gwamnan, Tsohon Shugaban Kasa Yakubu Gowon na wajen
taron. Haka Shugaban Majalisar Dattawa, Dr. Bukola Saraki da kuma Shugaban
Jam’iyyar APC mai mulki, Cif John Oyegun. Kai ba a bar manyan ‘Yan kasuwa
irinsu Alhaji Aliko Dangote a baya ba.
Sabon Gwamna Obaseki yayi
alkawarin cigaba da duk ayyukan da Tsohon Gwamna Oshiomole ya fara, ya kuma yi
alkwarin samar da ayyuka 200, 000 cikin wa’adin shekara hudu. Sabon Gwamna
Obaseki yace zai rike noma da harkar kasuwanci a Jihar. Obaseki yace zai dauki
harkar karatun mata da lafiyar su da muhimmanci. Ya kuma kira ‘Yan adawa da a
zo a hada kai.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment