Donald
Trump ba zai kyale Shugaba Buhari yayi abin da yake so ba-FFK
Femi Fani Kayode yace Shugaba Buhari na nema ya musuluntar da Najeriya
– Tsohon Ministan Kasar nan, Femi Fani-Kayode yace gara da Donald Trump ya lashe zaben Kasar Amurka
– FFK yake cewa Sabon Shugaban Kasar Amurka ba zai bar Shugaba Buhari ya musuluntar da Kasar nan ba
– Kayode ya taya Trump murna bayan ya fito daga tsari
Tsohon Ministan Sufurin
Jiragen sama na Kasar nan, Femi Fani-Kayode ya fito daga tsari kwanan nan. Bayan
fitowar sa, ya taya Sabon Shugaban Kasar Amurka da aka zaba, Donald Trump
murnar lashe zaben Kasar. Yace gara da Trump din ya kada Clinton.
Ko can dai Mista Kayode ya
dade yana goyon bayan Trump, ya taba wani rubutu a nan mai suna
‘Trump da kuma Musulunci’ inda yake cewa hamshakin Dan kasuwan nan Donald
Trump, zai lashe zaben Jam’iyyar sa ta Republican, kana kuma ya lashe zaben
Kasar Amurka inda za su kara da Hillary Clinton.
A wancan lokaci FFK
yace: ‘Duk da cewa mutane da dama ba za su yarda da ni ba har a Najeriya, amma
na tababa cewa Trump zai lashe zaben Amerika, kuma ina tare da shi. Mu (Yan
Najeriya) abin da muke so.'
Femi Fani-Kayode yace Trump
ba zai kyale a musuluntar da wata Kasa ba ko ya bar masu tsantsenin ra’ayin
addini suna abin da suka ga dama. Kayode yace Trump ne maganin Shugaba Buhari. Femi Fani-Kayode yake kuma
cewa Sabon Shugaban ba zai bari a ci gaba da keta hakkin bil adama ba
Kwanan nan ne dai Femi Fani Kayode ya fito daga Gidan tsari na Kuje, inda ya ce ya gana da Nnamdi Kanu da wasu 'Yan 'Boko Haram'. Da fitowar sa dai ya cigaba da sukar Gwamnatin Muhammadu Buhari kamar yadda ya saba.
No comments:
Post a Comment