– ‘Yan bindiga sun sace wani Tsohon Ministan Najeriya jiya a Garin Kaduna
– Wasu ‘Yan bindiga ne suka yi gaba da Ambasada Bagudu Hirse
– An kai wannan hari ne a Gidan Mamman Daura da ke Garin Kaduna
'Yan bindiga sun sace Ambasada Bagudu Hirse a gaban Gidan Mamman Daura
Jaridar Daily Trust ta
rahoto cewa an sace wani Tsohon Ministan Kasar nan a Gidan Alhaji Mamman Daura
da ke Garin Kaduna. Wasu ‘Yan bindiga ne dai da ba a san su ba, suka sace
Tsohon Ministan harkokin waje na Kasar, Ambasada Bagudu Hirse.
Wannan abu ya faru ne dai
jiya a gaban Gidan Alhaji Mamman Daura da ke kan Titin Inuwa Wada a cikin Garin
Kaduna. Ana zargin cewa Alhaji Mamman Daura yana gida a lokacin da wannan abu
ya faru. An ce ko a lokacin yana karbar ziyara daga ‘Yan uwa da abokan arziki.
Tsohon Ministan dai ya zo
Garin ne domin ta’aziyar rashin Marigayi Ibrahim Dasuki, tsohon Sarkin Musulmi.
Gidan Marigayi Dasuki bai da nisa da Gidan Alhaji Mamman Daura, don haka ne
Ambasadan ya tsaya don ya gaida Mamman Daura.
Wanda abin ya faru a gaban
sa, yace bayan Alhaji Bagudu ya fito daga mota tare da wani abokin sa, sai wasu
mutane kwatsam suka keto a guje a mota kirar Toyoto Corollo sun sha damara,
Nan-take suka ce ya shiga motar su, ko da ya tsaya wata-wata, sai suka harba
bindiga, tuni kowa ya tsere. Yanzu haka dai ba a san inda suka yi da shi ba. Jihar Kaduna dai ta zama abin da ta zama game da harkar rashin tsaro.
Sai
dai wata majiya ta nuna cewa an kai harin ne ga Abba Kyari, wanda shine
Shugaban Ma'ikatan Fadar Gwamnatin Tarayya, wanda na kusa da Alhaji
Mamman Daura ne, kuma ake sa ran yana gidan a lokacin. Ana dai zargin su
Mamman Daura sun rike madafan iko na Gwamantin Shugaba Buhari.
No comments:
Post a Comment