Tuesday, November 15, 2016

Ni ba barawo ba ne-Atiku Abubakar



Atiku Abubakar yace bai taba satar kudi ba...

Kai makaryaci ne...-El Rufai



– Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar yace shi ba barawo bane


– Atiku Abubakar yace El-Rufai mayaudari ne


– Sai dai Malam Nasiru El Rufai yace karya Atiku yake yi, idan ba tsoro ba, ya je Amurka mana

 

 


Alhaji Atiku Abubakar, Turakin Adamawa ya rike Mataimakin Shugaban Kasar nan na shekaru takwas, lokacin Shugaba Obasanjo. Alhaji Atiku Abubakar din ba da Dan Siyasa ne, hamshakin dan kasuwa ne. Atiku yace shi bai saci kudi ba game da wani sabon zargi da ake yi masa. 

A wata hira da Alhaji Atiku Abubakar yayi da Mujallar Hukumar EFCC mai yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya yace shi fa bai saci kudin kowa ba. Atiku Abubakar yace sharin da ake masa shine ya nada wasu Ministoci a lokacin Gwamnatin Obasanjo, Atiku Abubakar yace in dai wannan ne, ya wanke kan sa a Kotu.

Atiku Abubakar yace Kotu ta wanke sa sarai, don haka babu wanda ya taba samun sa da laifin sata a Kasar nan. Atiku Abubakar yace duk rikicin siyasa ne kurum ke kawo wannan maganganu. A littafin da Malam El Rufai ya rubuta, ya zargi Atiku Abubakar da laifuffuka na awon gaba da kudi, sai dai Atiku Abubakar din yace Nasir El Rufai bai kawo wata hujja ba.

Atiku Abubakar yace shi Malam Nasir El Rufai ne ma yayi kokarin kawo masa wasu hannun jari don ya karba, shi kuwa yace bai dace ba. Gwamna El-Rufai ya mayar da martani inda yace Atiku ya saba karya, idan kuma ya isa ya shiga Kasar Amurka idan ba a kama sa ba.


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...