An
yaye daliban ABU Zaria
– Jami’ar ABU Zaria ta yaye dalibai sama da 11,000 a karshen wannan makon
– Jami’ar ta yaye dalibai masu digiri da digirgir har ma da digir-digir
– Ciki an samu guda 49 da suka ciri tuta
Shugaban Jami'a, Farfesa Ibrahim Garba
Jami’ar Ahmadu Bello watau
ABU Zaria ta yaye dalibai a karshen wannan makon. Jami’ar da ita ce ta farko a
Arewacin Najeriya ta yaye dalibai masu digiri guda 11, 731.
Kamar yadda muka
samu labari akwai guda 2, 697 masu shaidar Digiri na biyu, sannan kuma guda 289
sun kammala karatun Digiri na uku watau Dakta. Ciki akwai guda 49 da suka ciri tuta, inda suka samu gamawa da mataki na farko watau 'first class'.
Shugaba Buhari ya ce za ayi
bincike game da irin badakalar da ake samu a cikin Jami’o’i. Shugaban Kasar
ya kuma yi kira da Jami’ar ta ABU Zaria da ta maida hankali wajen nazari game da
harkar noma. Farfesa Rasheed na Hukumar NUC ne ya wakilci Shugaban Kasar.
Shugaban Jami’ar Farfesa
Ibrahim Garba ya bayyana irin cigaban da Jami’ar ta samu wajen fanni
dabam-dabam a karkashin Shugabancin sa. ABU Zaria ta gina matatar
man fetur, sannan kuma ta gano wani maganin cutar malaria na ciwon sauro.
Farfesa Garba ya kira daliban da aka
yaye su zama masu tarbiya bayan ilmin da suka samu. Yanzu haka Jami'ar ABU Zaria ta yaye dalibai da dama a fadin duniya. Wannan ne dai karo na 39 da Jami'ar ta yaye daliban nata.
Muhammad Malumfashi daga Zaria
NAIJ Hausa
No comments:
Post a Comment