Thursday, November 17, 2016

‘Yan Najeriya fiye da 100 suka mutu a teku


Wasu ‘Yan Najeriya 27,500 sun shiga Kasar Italiya a sace




‘Yan Kasar Najeriya da dama sun isa Kasar Italiya ta barauniyar hanya



Mutane fiye da 27, 500 suka kaura zuwa Kasar Italiya ta teku



Da dama dai sun mutu a kan hanyar su zuwa can a halin yanzu

 

A cikin watan Jiya na Oktoba kadai, mutanen Najeriya da Kasar Eriteria fiye da 27,500 su ka shiga Kasar Italiya ta barauniyar hanya. Hukumar Turai mai lura da kan iyaka da ake kira Frontex ta bayyana haka.

Hukumar tace ba a taba samun irin wannan cin-ci-rindo ba haka a cikin lokaci guda. A ce a cikin wata guda kusan mutum 30,000 sun kaura zuwa Kasar ba tare da an sani ba. Da yiwuwar saboda kyawun yanayin ne jama’an wadannan Kasashe suka yi kaura zuwa Kasar ta Italiya domin kuwa lokacin da sanyi zai yi kamari, zai yi wuya a iya tsallakowa.

Mafi yawan masu hijiran dai ‘Yan Najeriya ne da kuma Kasar Eritrea. Sai dai an samu babbar matsala wajen haurowa, mutane fiye da 127 aka samu sun mutu a hanya garin tsallake teku.
Mafi yawan ‘Yan Najeriya da sauran ‘Yan Afrika da ke shiga Kasashen dai wahalar rayuwa ce ke kai su.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...