Friday, November 11, 2016

Duk rana ana cin abincin N3b a Legas-Gwamna Ambode





Gwamnatin Jihar Legas ta bayyana kokarin ta na ganin Jihar ta samu wadataccen abinci

 


Gwamna Ambode yace suna hada kai da wasu Jihohi wajen ganin ba a bar Legas a baya ba

 



Yanzu haka dai farashin man fetur yayi kasa, hakan ta sa ake ta fama a Kasar

 


Gwamnatin Jihar Legas ta Gwamna Ambode na kokarin ganin yadda Jihar za ta samu wadataccen abinci. Wasu Jihohin Kasar dai na fama da yadda za su biya albashi tun bayan da farashin man fetur ya ragu a duniya. Shi kuma Gwamna Ambode yana kokarin ganin yadda abinci zai samu ne a Jihar sa.

Gwamna Ambode ya bayyana cewa a duk rana ana cin abinci na sama da Naira Biliyan uku a Legas. Don haka ne Gwamna Ambode yace Legas ta shiryawa duk wanda zai zo kasuwancin kayan noma a Jihar. Gwamna Ambode yace ba dalili ace Najeriya tana shigo da kayan abinci a wannan lokaci.

Gwamna Ambode yayi wani taro tare da Alhaji Sani Dangote da sauran manyan masu kasuwancin kayan abinci. Taken taron dai ya kunsa yadda Legas za ta wadatu ne da abinci. Gwamna Ambode yace Jihar sa ta hada kai da Kebbi wajen noman shinkafa da su masara. Ambode yace tana nan kawai Jihar Legas za ta samu duk abincin da za ta ci.

Haka ma dai Audu Ogbeh yace Gwamnatin Tarayya za ta shigo da manyan kayan aikin shinkafa wanda za su taimaka wajen ganin Kasar ta noma shinkafa da za ta ci da kan ta nan da shekaru biyu masu zuwa. Ministan noma yace Gwamnatin Tarayya za ta kawo manyan na’urorin casar shinkafa guda 40 cikin Kasar.

Gwamna Ambode yace Jihar Legas ta nemi filin noma a Garuruwa irin su Ogun, Oyo, da Abuja domin noman shinkafa da su kwakwan manja.


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...