– Shugaba Buhari yayi farin ciki bayan da Kungiyar Super Eagles ta ci wasan ta
– Shugaban Kasar, Muhammadu Buhari ya aika sakon jinjina ga ‘Yan kwallon kafar Kasar
– Shugaba Buhari ya godewa Jihar Akwa Ibom da sauran ‘Yan kallo
Shugaba Buhari yayi farin
cikin ganin Kungiyar Kwallon Kafar Super Eagles tayi nasara a wasan ta da ta
buga jiya. Super Eagles na Najeriya sun doke Kasar Algeria da ci 3-1 a wasan
zuwa cin Kofin duniya na shekarar 2018 a Kasar Russia.
Shugaba Buhari ya aika
wannan sako ne ta daya daga cikin masu ba sa shawara game da harkokin yada
labarai, Mista Femi Adesina. Shugaba Buhari yace ‘Yan Super Eagles din ba su ba
da kunya ba. Shugaba Buhari ya tabbatarwa Kungiyar Kwallon Kafan Kasar masu
maki shida a zagayen, cewa mutanen Kasar na goyon bayan su dari-bisa-dari.
Shugaba Buhari ya kuma mika
godiyar sa ga Gwamnatin Jihar Akwa Ibom inda aka buga wasan. An doka wasan ne a
filin wasa na Godswil Akpabio da ke Birnin Uyo na Jihar. Shugaba Buhari ya kuma
godewa ‘Yan kallo da magoya bayan Kungiyar.
Kasar Najeriya ta doke Kasar
Algeria ne da ci 3-1, ‘Yan wasan Kungiyar Chelsea; Victor Moses da Kyaftin
Mikel Obi suka ci kwallayen. Victor Moses ya zuba kwallaye har biyu a wasan.
Yanzu Kasar Najeriya ce a kan gaba a rukunin na ta na zuwa Gasar cin kofin
duniya da za a buga a Kasar Russia.
No comments:
Post a Comment