Tuesday, November 1, 2016

Abin Mamaki: wanda aka ba tsaro yayi sata





Kotu a Abuja ta kama wani mai gadi yayi sata

 


Kotun da ke Ubguwar Area I a Birnin Tarayya ta bada belin wanda ake zargi

 


court (1)



Wani Kotu da ke zama a Unguwar Karmo da ke Area 1 a Babban Birnin Tarayya Abuja, ta bada belin wani saurayi da ake zargi da laifin yayi sata. Ana zargin wannan saurayi da bai wuce shekaru 19 ba ya sace kayan ginin gidan da yake gadi a Garin na Abuja.

Alkalin Kotun na Area 1, Abubakar Sadiq ya bada belin wannan mai gadi mai suna Peter Gwaza Inji Jaridar Daily Trust. An bada belin na sa ne a kan kudi har N500,000 tare da kawo wanda zai tsaya masa. 


Kotun tace dole wanda zai tsayawa wannan mai gadi da ake zargi da lafin sata ya zama ma’aikacin Gwamnati, kuma wanda yake akalla mataki na 7 na aiki. Yanzu haka dai an daga shari’ar zuwa 10 ga wannan wata. An bayyana cewa dai wanda ake zargi ya bayyana cewa ya saci kayan da ake magana, har ma ya sayar da su tuni kan kudi N17,000.

Ku karanta cikakkun labarai a shafin NAIJ Hausa

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...