Wednesday, November 2, 2016

Kasuwar kwadi tana ci a Jihar Kano




Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Kano yayi alkawarin taimakawa kasuwar kwadi a Jihar Kano

 



Masu kwadi suna cin Karen su ba babbaka a Jihar Kano

 



Jama’a da dama yanzu an ganewa naman kwadi


Frog is a delicacy in some parts of Nigeria


Dr. Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano ya tabbatar da cewa Gwamnatin sa za ta taimakawa masu harkar naman kwadi a Jihar Kano. Jaridar Premium Times ta gano cewa dai yanzu naman kwadi sun zama abin da suka zama. 

Masu kwadi a Jihar Kano dai da ma wasu Yanki na Arewacin Kasar suna cin Karen su ba tare da babbaka ba a halin yanzu, don kuwa mutane da dama yanzu sun ganewa naman kwadi a Kasar nan. Yanzu haka, an gano wata kasuwa a Kadawa da ke Karamar Hukumar Garun Malam a Jihar Kano da ke da kasuwar kwadi.

Yanzu haka dai ‘Yan kasuwa da dama sun shiga wannan Gari na Garun Malam domin wannan kasuwanci na gyara naman kwadi. Ko dama can dai ba yau aka fara harkar gyara naman kwadi ba inji masu abin. Wani dan kasuwan yace ana sayar da guda daya kusan N200. 

A karanta labaran mu a shafin NAIJ Hausa

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...