Ashe
‘Yan Najeriya ba su da imani?
– An kona wani karamin yaro kurmus a Legas wai don ya saci Garin Rogo
– Yaron dai bai wuce shekara 7 ba a duniya
– Wasu ‘Yan Najeriya suna ganin duk laifin Shugaba Buhari ne
A Garin Legas ma wani
mummunan abu ya faru kwanan nan, inda wani sabon bidiyo ya bayyana. Idan dai ta
tabbata, wasu’Yan Najeriya suka kona wani yaro karami dan shekara 7 har ya mutu
don ya saci Garin rogo.
Wani daga cikin wanda abin
ya faru a gaban sa, ya dauki bidiyo. Babu dai wanda yayi kokarin agazawa yaron
kar a kashe shi, haka dai yayi ta konewa
har ya isa lahira. Ana zargin yaron da satar Garin rogo ne dai, hakan ta sa
mutane suka dauki doko a hannun su.
Sai dai wasu ‘Yan Najeriya
suna ganin cewa duk Shugaba Buhari ya jawo wannan hali da ake ciki. Masu amfani
da hanyoyin sadarwa na zamani na Facebook da Twitter suka ce duk yunwar da
Shugaba Buhari ya jefa Kasar ne ya kai ga wannan.
Yanzu haka dai ana neman
Jami’an ‘Yan Sanda suyi bincike domin gano wadanda suka yi wannan aiki su
hukunta su. Ba yau dai 'Yan Najeriya suka fara daukar doka a hannun su ba, manyan barayi kuma sai yadda suka ce za ayi.
Wannan ai koh mutan jahiliyya ba su wannan haukan
ReplyDelete