Tuesday, November 22, 2016

Wani Dan Najeriya zai je har Kasar Ingila da kafa



Tun daga Kaduna, wani mutumi zai yi tattaki zuwa Birtaniya


 

Wani mutumi zai yi tattaki daga Garin Kaduna zuwa Kasar Birtaniya


Wannan mutumi ya fara tafiyar ne Ranar Lahadi 20 ga wannan  wata


Wannan mutumi zai yi wani tattaki ne domin jawo hankalin mutanen duniya game da ta’addanci

 

Wani mutumi ya kama shirin tattaki daga Garin Kaduna, kuma ba zai tsaya ko ina ba sai Kasar Ingila. Wannan mutumi zai yi wannan tafiya ne a kafa saboda ya jawo hankalin mutanen Duniya game da harkar ta’addanci.

Wannan matafiyi mai suna Abubakar Duduwule zai bi ta Jihar Neje ne, daga nan sai Garin Abuja, shikenan sai ya zarce har Kasar Birtaniya, inda zai tsaya. Kuma dai zai yi wannan tafiya ne duk a kafa. 

Duduwule yace ya zagaye kaf Arewa yana yada zaman lafiya da rashin fitina da kuma illar shaye-shaye. Yace ya kamata yanzu ya shiga Duniya. Abubakar Duduwule yace tun shekarar 2008 ya fara irin wannan tattaki.

Shekarun baya dai Abubakar Duduwule ya ja kafa har Kasar Kamaru daga Jihar Adamawa. Duduwule dai yana kokarin yada sakon yaki da ta’addanci a ne a duniya, hakan ta sa zai taka da kafar sa har Kasar Birtaniya.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...