Sarkin
Musulmi bai san yadda abin yake ba-Gwamna Ortom
– Gwamnan Jihar Benue yace Sarkin Musulmi ya jahilci dalilin bude filin jirgin sama a Jihar
– Kwanakin baya Sarkin Musulmi yace bai dace a bude filin jirgin sama ba
– Sai dai Gwamnan na Benue yace duk wanda ya fadi haka jahili ne ko wanene
Gwamnatin Jihar Benue ta
kare kan ta da yunkurin bude filin saukar jirgin sama a Jihar. Gwamna Ortom
yake cewa duk wanda ya soki maganar bude filin jirgin sama a Jihar to jahili
ne, bai fahimci lamarin Jihar ba ko kuma hassada ce kurum, kuma komai ilmin
mutum.
Kwanakin baya kadan Sarki
Musulmi, Abubakar Sa’ad yake cewa bai dace a rika gina filayen saukan jiragen
sama ba, yayin da ake fama da hanyoyin titi a Kasa marasa kyau. Gina filin
jirgin sama dai yana da matukar tsada, bayan jama’a da dama ma mutuwa a
hanyoyin Kasa.
Shi dai Gwamna Ortom bai ji
dadin wannan magana ba, yace Sarkin Musulmi bai fahimci lamarin bay a tsoma
baki.
Mafi yawan mutane dai ba su
cika hawa jiragen sama ba a Yankin, ko ka ga akwai filin saukar jirgi a
makwabta. An fi hawa motoci, sau dama sai ka ga an kashe kudi alhali ba a
amfani da filyane jirgin. Yayin da tituna ke bukatar gyara
No comments:
Post a Comment